ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bukaci ‘Yansanda Da Likitocin Dabbobi Su Samar Da Tsaro Ga Fannin Kiwon Dabbobi

by Abubakar Abba and Sulaiman
8 months ago
Dabbobi

Ministan Ma’aiktar Bunkasa Kiwo, Idi Mukhtar Maiha, ya yi kira ga kwararrun Likitocin Dabbobi da ke aiki a Rundunar ‘yansanda, da su yi kokari wajen bai wa fannin kiwon dabbobi kariyar da ta kamata.

Maiha, ya bayar da wannan shawarar ce; a taron bita ta wayar da kai na kwana biyu a Abuja da aka shirya, karkashin shirin aikin tallafawa da dogaro da kai na kiwo (L-PRES).Ya yi kira a gare su da su yi amfani da kwarewarsu wajen sanya ido kan dakile yaduwar cututtukan da ke kama dabbobi da yin gangamin wayar da kai kan yi wa dabbobi allurar rigakafin kamuwa da cutuka tare da taimakawa wajen magance rikice-rikice a tsakanin manoma da Fulani Makiyaya.

  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Kiran Taron Wakilan Gamayyar Kungiyoyin Masu Aikin Sa Kai Ta Kasar Sin Karo Na 3
  • PRP Ta Gargadi Sabon Shugaban PDP Kan Neman Taimakon Kasashen Waje A Rikicin Jam’iyya

Ministan ya jaddada muhimmancin tura kwararrun likitocin dabbobin aikin na ‘yansanda, musamman domin taimakawa wajen kara karfafa kula da lafiyar dabbobi da kuma kara karfafa tsaro “Duba da yadda ake da sama da kwararrun likitocin dabbobin 80 da kuma sauran kwararru sama da 70 a cikin aikin na ‘yansanda a kowace jiha a kasar, gudanmawarku a fannin, na da matukar muhimmanci “.

ADVERTISEMENT

Kazalika, Mukhtar ya kuma bukaci Babban Shugaba a Cibiyar Kula da Kiwon Lafiyar Dabbobi ta Kasa (CBON), Samuel Anzaku, ya tabbatar da cewa; likitocin dabbobin ‘yansanda, sun shiga cikin aikin gangamin yi wa dabbobi allurar rigakafi gadan-gadan tare da ci gaba da gudanarwa a daukacin fadin kasar nan da kuma kara sanya ido kan dakile yaduwar cututtukan dabbobi da ke shigowa ta iyakokin wannan kasa.

Ita kuwa a nata jawabin, Mataimakiyar Babban Sifoto na ‘yansanda, AIG Aishatu Baju Abubakar, wadda kuma ta wakilce shi a wajen taron, Sifetan ya yaba da irin salon shugabancin ministan tare kuma da yabawa kan yin hadakar a karkashin shirin na L-PRES, inda ya bayyana cewa; hakan zai taimaka wajen kara samar da wadataccen abinci a kasar da kuma kara wanzar da zaman lafiya a tsakanin al’umma.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Shi kuwa a nasa jawabin, Babban Shugaba a Cibiyar Kula da Kiwon Lafiyar Dabbobi ba Kasa (CBON), Samuel Anzaku ya zayyano irin kokarin da cibiyar ke ci gaba da yi, na dakile yaduuwar cututtukan dabbobi a daukacin fadin kasar. Shi ma a nasa bangaren, a jawabinsa na maraba a madadin jami’in shirin na kasa, Mustapha Mohammad, ya shawarci mahalarta taron da su karara yin aiki da sauran hukumomin gwamnati, domin cimma burin da aka sanya a gaba.

Dabbobi
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”
Dabbobi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Hatsarin Tankar Mai Da Gobara Sun Yi  Ajalin Mutum 3 A Kano

Hatsarin Tankar Mai Da Gobara Sun Yi  Ajalin Mutum 3 A Kano

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.