Gwamnatin Nijeriya na ƙara ƙoƙarin bunƙasa ɓangaren ma’adinai ta hanyar jawo masu zuba jari, da fasaha da ƙwarewa daga ƙasar Turkiyya domin haɓaka albarkatun ma’adinai. Wannan na zuwa ne bayan ƙasashpen biyu sun rattaba hannu kan yarjejeniyar haɗin gwuiwa a fannin ma’adinai.
Ministan Raya Ma’adinai, Dr. Dele Alake, ya ce yarjejeniyar za ta taimaka wajen faɗaɗa bincike da sarrafa ma’adinai a Nijeriya, inda ya bayyana cewa duk da an yi bincike ne a ƙasa da kashi 5 cikin 100 na faɗin ƙasar, an gano sama da nau’ikan ma’adinai masu muhimmanci 44 da suka haɗa da lithium, da cobalt, da nickel, da tin da sauransu.
Alake ya ce daga cikin muhimman abubuwan da yarjejeniyar ta ƙunsa akwai musayar fasaha, da horas da ƙwararru, da jawo jarin ƙasashen waje da kuma kare muhalli. Ya jaddada cewa Nijeriya ba ta son ci gaba da fitar da ɗanyen ma’adinai kawai, sai dai tana son a sarrafa su a cikin gida domin ktara darajarsu da kuɗaɗen shiga.
Ministan ya kuma yi kira ga masu zuba jari na Turkiyya su yi anfani da sabbin sauye-sauyen da gwamnati ta aiwatar a ɓangaren ma’adinai, ciki har da tsarin lasisi na zamani ta yanar gizo. Ya ce ƙasashen biyu sun kafa kwamitocin fasaha domin tabbatar da aiwatar da yarjejeniyar cikin gaggawa da kuma ƙarfafa haydin gwuiwar tattalin arziƙi tsakanin Nijeriya da Turkiyya.















Discussion about this post