Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kashe mutane biyar a wani sabon hari da suka kai a ƙauyen Tse Ameen da ke yankin Mbapa, ƙaramar hukumar Gwer ta yamma a Jihar Benuwe.
A cewar mazauna yankin, waɗanda ake zargin sun kai harin ne a daren ranar Asabar, inda suka afkawa al’ummar ƙauyen ba zato ba tsammani.
Wani mazaunin yankin da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa manema labarai ta wayar tarho a ranar Litinin cewa, an gano gawawwaki biyar a ranar Lahadi, yayin da wasu da dama har yanzu ba a san inda suke ba.
ADVERTISEMENT
Ya ce, “An gano gawawwaki biyar, ciki har da maza uku da mata biyu, a jiya (Lahadi).”















Discussion about this post