ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Koro Ƴan Nijeriya 366 Daga Kanada, Wasu 974 Na Fuskantar Korar

by Abubakar Sulaiman
7 months ago

Hukumar kula da iyakokin Kanada (CBSA) ta kora ’yan Nijeriya 366 daga ƙasar tsakanin Janairu zuwa Oktoban 2025, yayin da matakan tilasta dokokin shige da fice suka kai matsayi mafi tsauri cikin fiye da shekaru goma. Bayanai sun kuma nuna cewa ’yan Nijeriya 974 na cikin jerin mutanen da ake shirin kora daga Kanada a halin yanzu.

Ƙididdigar, wadda aka sabunta a ranar 25 ga Nuwamba, 2025, ta nuna cewa Nijeriya ta zo ta tara a cikin ƙasashe 10 da aka fi korar ƴan ƙasarsu daga Kanada a wannan lokaci, yayin da ta zo ta biyar wajen yawan mutanen da ke fuskantar korar da ke ci gaba. Hakan na nuna ƙaruwar tsauraran matakai kan baƙin haure a ƙasar.

  • Sin Ta Fitar Da Sakamakon Bincike Game Da Yadda Kanada Ke Nuna Wa Kayayyakinta Wariya
  • NIS Ta Ƙaddamar Da Sabon Ingantaccen Fasfo A Ƙasar Kanada

Binciken bayanan ya nuna cewa adadin ƴan Nijeriya da ake korar su ya bambanta a tsawon shekaru. A 2019 an kori 339, adadin ya ragu zuwa 302 a 2020, 242 a 2021, sannan 199 a 2022. Bayan rashin bayyana a jerin manyan ƙasashe a 2023 da 2024, Nijeriya ta koma jerin a 2025 da mutane 366 cikin watanni 10, ƙarin kashi takwas cikin ɗari idan aka kwatanta da 2019.

ADVERTISEMENT

Rahoton ya ce hakan na faruwa ne yayin da Kanada ke korar kusan baki 400 a kowane mako, inda a shekarar kasafin kuɗi ta 2024–2025 aka kori mutane 18,048 da kuɗin kusan dala miliyan 78.

Dokar shige da fice ta Kanada ta tanadi nau’o’in umarnin korar mutum uku—barin ƙasa cikin kwanaki 30, hana dawowa na tsawon lokaci, ko kuma korar dindindin—inda galibin waɗanda ake kora su ne ƴan neman mafaka da suka gaza cike ƙa’ida.

LABARAI MASU NASABA

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu
  • Abubakar Sulaiman
    Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano
  • Abubakar Sulaiman
    An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

MASU ALAKA

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON
Labarai

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu
Labarai

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau
Rahotonni

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Next Post
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Hukumar Kula Da Alkalai Ta Haramta Wa Lauyoyi 34 Zama Masu Shari’a A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.