ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Maka El-Rufai Da Wasu 13 A Kotu Kan Nada Sarkin Zazzau, Ahmed Nuhu Bamalli

by Abubakar Abba
3 years ago
El-Rufai

Tsohon Wazirin masarautar Zazzau, Alhaji Ibrahim Muhammad Aminu, ya maka Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai, masarautar Zazzau da kuma wasu mutane 12 a gaban babbar kotun jihar.

Aminu, ya maka su ne a gaban kotun a kan nada Ahmed Nuhu Bamalli a matsayin sarkin Zazzau na 19.

  • Da Dumi-Dumi: Jakadan Nijeriya A Sifaniya, Demola Seriki Ya Rasu
  • Karancin Mai: IPMAN Ta Yi Barazana Rufe Gidajen Mai Saboda Gargadin DSS 

Aminu, wanda na daya daga cikin masu nada sarki a masarautar Zazzau, ya bukaci kotun ta soke martaba Ahmed Nuhu Bamalli a matsayin sarkin Zazzau.

ADVERTISEMENT

Da aka gabatar da kakar a jiya Laraba wasu daga cikin wadanda Aminu ya maka a gaban kotun akwai sarkin da marigayi Limamin Kona, Malam Sani Aliyu, wand a ya rasu a watan Yulin 2022.

El-Rufai ne dai nada Bamalli a matsayin sabon sarkin ne a ranar 7 ga watan Okutobar 2020, wanda a baya ya kasance jakadan Nijeriya ne a kasar Thailand.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

A lokacin da aka gabatar da karar a jiya, alkalin kotun mai shari’a Isah Aliyu, ya dage sauraron karar zuwa ranar 23 ga watan Fabirairun 2023 don a bai wa lauyan wanda ake kakar damar yin nazari a kan karar tare da kuma gabatar wa da kotun hujjarsa a kan karar.

A tattaunawarsa da manema labarai jim kadan bayan zaman kotun, lauyan da ke tsayawa mai karar Barista Rabiu Saidu, ya ce, wanda yake tsayawa ya shigar da kakar ne saboda sauran wadanda suka kasance masu nada sarki, ba a ba su damar zabo wanda zai zama sarkin ba, inda hakan ya sabawa ala’adar nasarautar.

Ya kara da cewa, a bisa ka’ida masu zabo wanda zai zama sarkin, na tura wa gwamna sunayen wadanda za a nada a matsayin sarkin masarautar, inda ya ce, wanda a yanzu yake a kan karagar masarautar, sunansa baya a cikin sunayen da aka turawa gwamnan, saboda haka bai dace a nada shi sarkin ba, domin nadinsa, ya saba wa shawarar da masu zabo sarkin suka bayar.

Lauya mai tsaya wa masarautar Zazzau, Barista Aminu Usman Bamalli, ya ce, lauyan mai karar ya kamata ya gabatar da adireshin da zai kasance shi mazaunin ne a Kaduna kamar yadda doka ta 4 da ta 6 a tsarin aikin kotun jihar ta tanadar, inda ya ce, amma lauyan, ya kasance mazaunin Abuja ne kuma hakan zai yi matukar wahala a gare su wajen gabatar masa da takardunsu a kan lokaci.

Kotun ta dage sauraren karar zuwa ranar 23 ga watan Fabirairun 2023.

El-Rufai
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Jirgin Kasa Ya Yi Awon Gaba Da Mota Dauke Da Fasinjoji A Abuja

Jirgin Kasa Ya Yi Awon Gaba Da Mota Dauke Da Fasinjoji A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.