A jiya Litinin ne aka gudanar da kasaitaccen bikin cika shekaru 66 da samun ’yancin kan kasar Togo, inda yayin bikin aka gudanar da gagarumin faretin sojoji da jerin-gwanon fararen hula.
Shugaban kasar Togo, Jean-Lucien Savi de Tove, da shugaban majalisar ministocin kasar Faure Gnassingbe, da sauran manyan baki, da wakilai daga sassa daban daban, da jami’an ofisoshin jakadancin kasashe daban saban sun halarci bikin.
Kazalika, a karon farko a yayin wannan biki, dalibai cikin wata tawaga daga kwalejin Confucius dake jami’ar Lome, sun yi tattaki tare da nuna al’adun gargajiyar kasar Sin.
An kuma gayyaci jakadiyar kasar Sin a Togo Wang Min, domin ganewa idanunta yadda wannan gagarumin biki ya wakana.
Game da hakan, jakadiyar ta Sin ta shaidawa kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua cewa, “Jan launi na Sin” ya yi fice yayin bikin, inda ya kara kayata nune-nunen al’adun gargajiya na kasar Togo, tare da haskaka irin kyakkyawar musaya dake gudana tsakanin wayewar kai irin na Sin da na Togo. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post