ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Rage Hukuncin Kwashe Maki 10 Da Aka Yi Wa Everton

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Everton

An rage hukuncin da aka yanke wa Ebeton kan saba wa dokokin hada-hadar kudi ta gasar Premier daga maki 10 zuwa shida bayan nasarar da kungiyar ta yi a karar da ta daukaka.

An gurfanar da kungiyar a gaban wata hukuma mai zaman kanta a watan Maris bisa zargin tafka laifukan a kakar wasa ta 2021 zuwa 20022, kuma da farko an cire mata maki 10 a watan Nuwamban 2023.

  • Pogba Zai Ɗaukaka Ƙara A Kan Dakatar Da Shi Daga Buga Ƙwallo Na Tsawon Shekaru 4
  • Liverpool Ta Lashe Kofin Carabao Karo Na 10 Bayan Doke Chelsea A Wembley

Ragin da aka yi kan hukuncin zai sa Everton ta kasance da maki 25 sannan ta koma mataki na 15 a teburin Premier bayan wata sanarwa da hukumar tafiyar da gasar Premier League ta fitar inda ta bayyana cewa “Hukumar daukaka kara mai zaman kanta ta yanke cewa hukuncin da Everton FC za ta fuskanta kan keta ka’idojin kasuwanci na Premier League na kakar 2021 zuwa 2022, zai zama cire mata maki shida nan take.

ADVERTISEMENT

Hukumar ta ce wannan ya biyo bayan daukaka karar da Everton ta yi na hukuncin da wata hukuma mai zaman kanta ta yanke a watan Nuwamba 2023 na cire maki 10 saboda keta dokokin.

Sanarwar ta kara da cewa wannan hukuncin da aka sake wa fasali zai fara aiki ne nan take kuma za a sabunta teburin Premier daga lokacin da aka yi hukuncin domin yin la’akari da hakan.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Hukuncin farko da aka yanke wanda shi ne mafi girma a tarihin gasar Premier – ya sa Everton ta rikito daga mataki na 14 zuwa 19 a kan teburi amma kuma duk da haka kungiyar ba ta karaya ba, ta dage wajen samun nasara a wasanni.

Har Yanzu Everton da Nottingham Forrest Ba Su Da Makoma Amma kuma har yanzu kungiyoyin kwallon kafa na Everton da Nottingham Forest ba za su iya sanin makomarsu ba har sai bayan kammala gasar Premier ta bana saboda bincike da ake ci gaba da yi.

Everton na murnar rage hukuncin da aka yanke mata daga maki 10 zuwa maki shida bayan ta daukaka kara amma duk da haka Everton da Forrest na da sabbin tuhume-tuhume da ake yi masu sakamakon keta dokokin hada-hadar kudi na gasar Premier League, inda za a gurfanar da kungiyoyin biyu a gaban wani kwamiti mai zaman kansa a farkon watan Maris, kuma dole ne su tabbatar da hukunci kafin ranar 8 ga Afrilu.

Idan har an yanke hukuncin cire maki, kungiyoyin biyu na da kwanaki bakwai domin daukaka kara, sannan dole ne a tabbatar da sakamakon wannan lamari kafin babban taron gasar Premier League wanda za a gudanar a ranar 24 ga watan Mayu, kwana biyar bayan an kammala kakar wasa ta bana.

Hakan na nufin cewa idan har kugiyoyin biyu sun fuskanci hukuncin cire maki suna iya samun kansu a matakin gasar ‘Championship’ ko da kuwa sun kai labari sakamakon wasannin da suka buga a kakar wasa ta bana.

Everton
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
Xi Ya Jaddada Bukatar Raya Sabon Makamashi Mai Inganci A Kasar Sin

Xi Ya Jaddada Bukatar Raya Sabon Makamashi Mai Inganci A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.