ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Rage Hukuncin Kwashe Maki 10 Da Aka Yi Wa Everton

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Everton

An rage hukuncin da aka yanke wa Ebeton kan saba wa dokokin hada-hadar kudi ta gasar Premier daga maki 10 zuwa shida bayan nasarar da kungiyar ta yi a karar da ta daukaka.

An gurfanar da kungiyar a gaban wata hukuma mai zaman kanta a watan Maris bisa zargin tafka laifukan a kakar wasa ta 2021 zuwa 20022, kuma da farko an cire mata maki 10 a watan Nuwamban 2023.

  • Pogba Zai Ɗaukaka Ƙara A Kan Dakatar Da Shi Daga Buga Ƙwallo Na Tsawon Shekaru 4
  • Liverpool Ta Lashe Kofin Carabao Karo Na 10 Bayan Doke Chelsea A Wembley

Ragin da aka yi kan hukuncin zai sa Everton ta kasance da maki 25 sannan ta koma mataki na 15 a teburin Premier bayan wata sanarwa da hukumar tafiyar da gasar Premier League ta fitar inda ta bayyana cewa “Hukumar daukaka kara mai zaman kanta ta yanke cewa hukuncin da Everton FC za ta fuskanta kan keta ka’idojin kasuwanci na Premier League na kakar 2021 zuwa 2022, zai zama cire mata maki shida nan take.

ADVERTISEMENT

Hukumar ta ce wannan ya biyo bayan daukaka karar da Everton ta yi na hukuncin da wata hukuma mai zaman kanta ta yanke a watan Nuwamba 2023 na cire maki 10 saboda keta dokokin.

Sanarwar ta kara da cewa wannan hukuncin da aka sake wa fasali zai fara aiki ne nan take kuma za a sabunta teburin Premier daga lokacin da aka yi hukuncin domin yin la’akari da hakan.

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

Hukuncin farko da aka yanke wanda shi ne mafi girma a tarihin gasar Premier – ya sa Everton ta rikito daga mataki na 14 zuwa 19 a kan teburi amma kuma duk da haka kungiyar ba ta karaya ba, ta dage wajen samun nasara a wasanni.

Har Yanzu Everton da Nottingham Forrest Ba Su Da Makoma Amma kuma har yanzu kungiyoyin kwallon kafa na Everton da Nottingham Forest ba za su iya sanin makomarsu ba har sai bayan kammala gasar Premier ta bana saboda bincike da ake ci gaba da yi.

Everton na murnar rage hukuncin da aka yanke mata daga maki 10 zuwa maki shida bayan ta daukaka kara amma duk da haka Everton da Forrest na da sabbin tuhume-tuhume da ake yi masu sakamakon keta dokokin hada-hadar kudi na gasar Premier League, inda za a gurfanar da kungiyoyin biyu a gaban wani kwamiti mai zaman kansa a farkon watan Maris, kuma dole ne su tabbatar da hukunci kafin ranar 8 ga Afrilu.

Idan har an yanke hukuncin cire maki, kungiyoyin biyu na da kwanaki bakwai domin daukaka kara, sannan dole ne a tabbatar da sakamakon wannan lamari kafin babban taron gasar Premier League wanda za a gudanar a ranar 24 ga watan Mayu, kwana biyar bayan an kammala kakar wasa ta bana.

Hakan na nufin cewa idan har kugiyoyin biyu sun fuskanci hukuncin cire maki suna iya samun kansu a matakin gasar ‘Championship’ ko da kuwa sun kai labari sakamakon wasannin da suka buga a kakar wasa ta bana.

Everton
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
Xi Ya Jaddada Bukatar Raya Sabon Makamashi Mai Inganci A Kasar Sin

Xi Ya Jaddada Bukatar Raya Sabon Makamashi Mai Inganci A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.