ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

by Abubakar Abba
3 weeks ago
Jujin

Ana ci gaba yin suka, kan yadda wasu kamfanonin ketare da ke shigo da Kwantaina da babu wasu kaya a cikinsu zuwa cikin kasar, wadanda  kuma ake jibgesu, a duk inda suka ka dama.

Wannan batun wanda a yanzu,  wasu kwararru a fannin sun fara  kira ga mahukunta a kasar, da sanya a fara gudanar da binciken kan jibge Kwantainar, ba bisa bin ka’ida da kamfanobin suka shafr shekaru suna yi, hakan ya sanya hukumar Kustam rasa samun kudaden shiga da suka kai yawan dala miliyan 600.

Wasu daga cikin kwararru a fannin hahada-hadar sufurin Jiragen Ruwa a kasar nan ne, suka bayyana hakan.

ADVERTISEMENT

Daya daga cikinsu, Mista Okey Ibeke,  ya yi kira ga hukumar Kwastam ta kasa  da ta binciki yadda ake shigowa da Kwantainar daga waje tare da kuma sayar da su a cikin kasar nan.

Ibeke wanda ya bayyana haka a taron manema labarai a jihar Legas, ya yi gargadi da cewa, lamarin na janyowa hukumar rashin samun kudaden shiga.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

Ya buga misali da wasu rahotannin da ke nuna cewa, daya daga cikin irin wadannan kamfanonin da ke aikinsu a cikin kasar, na shirin fara saayar da wasu Kwantaina guda  2,500 da babu wasu kaya a cikinsu a kasar nan.

A cewarsa, an ruwaito cewa, kamfanin, zai sayar da kowacde daya, kan farashi daga dala 1,600 zuwa dala 2,000 ,inda masu sayen za su tura kudaden zuwa cikin wani Asusun kamfanin da ke a kasar Amurka.

Ya kara da cewa, wannan harkallar, na ci gaba da diga alamar tambaya, ta rashin bin ka’idojin hukumar Kwastam, kan shigo da irin wadannan Kwantaina da kamfanoni na kasar waje ke yi, zuwa cikin kasar nan.

” A bisa tsarin yarjejeniyar wucin gadi ta shigo da Kwantaina cikin kasar nan tare cire masu shinge, za a iya kara shigo da su ne kawai idan an yi amfani da su, gabanin a hukumance a fara sayar da su a cikin kasar, wanda kuma hakan, zai iya kasancewa, bayan hukumar Kwastam, ta tantance su da tsarin biyan kudade fito da kuma na biyan haraji, kan kayan, “A cewarsa.

” Duk wata hada-hadar da aka yi, ba tare da bin wadannan ka’idojin ba, tamkar take hukumarKwastam ta shekarar 2023 ne, musamman duba da cewa, shigo da su ba bisa ka’ida ba, na janyo zurarewa samar da kudaden shiga, da ya kamata Gwamnatin Tarayya ta samu,’ Inji shi.

Ya ci gaba da cewa, hakan janyowa Gwamnatin Tarayya, asarar samun kudaden shiga na fito da suka kai daga dala 350 zuwa dala 400  da kuma kudaden haraji a duk Kwantaina daya.

Ya yi nuni da cewa, bisa rashin samar da kwakyawan tsari a kasar nan a hada-hadar kasuwanci, hakan na kara mayar da kasar, jujin jibge irin wadannan Kwantaina.

Kazalika, ya yi nuni da cewa, hakan zai kuma haifar da cikas, ga kokarin da Babban Bankin Nijeriya ke ci gaba da yi na kara karfafa darajar Naira a kasar nan musamman domin a rage dogaro kan kudaden musaya na kasar waje.

Ya bayyana cewa, ya kamata shugaban hukumar Kwastam na kasar, ya gaggauta dakatar da ci gaba da sayar da Kwantaina na wucin gadi tare da gudanar da cikakken bincike.

Ya bayyana cewa daukar matakai sune kawai mafita kan wannan matsalar, musamman domin a dakile yadda kudaden shiga na Gwamnatin Tarayya ke zurarewa zuwa wata hanya.

Jujin
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha'aban Bisa Taurin Bashi

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.