Ana ci gaba yin suka, kan yadda wasu kamfanonin ketare da ke shigo da Kwantaina da babu wasu kaya a cikinsu zuwa cikin kasar, wadanda kuma ake jibgesu, a duk inda suka ka dama.
Wannan batun wanda a yanzu, wasu kwararru a fannin sun fara kira ga mahukunta a kasar, da sanya a fara gudanar da binciken kan jibge Kwantainar, ba bisa bin ka’ida da kamfanobin suka shafr shekaru suna yi, hakan ya sanya hukumar Kustam rasa samun kudaden shiga da suka kai yawan dala miliyan 600.
Wasu daga cikin kwararru a fannin hahada-hadar sufurin Jiragen Ruwa a kasar nan ne, suka bayyana hakan.
Daya daga cikinsu, Mista Okey Ibeke, ya yi kira ga hukumar Kwastam ta kasa da ta binciki yadda ake shigowa da Kwantainar daga waje tare da kuma sayar da su a cikin kasar nan.
Ibeke wanda ya bayyana haka a taron manema labarai a jihar Legas, ya yi gargadi da cewa, lamarin na janyowa hukumar rashin samun kudaden shiga.
Ya buga misali da wasu rahotannin da ke nuna cewa, daya daga cikin irin wadannan kamfanonin da ke aikinsu a cikin kasar, na shirin fara saayar da wasu Kwantaina guda 2,500 da babu wasu kaya a cikinsu a kasar nan.
A cewarsa, an ruwaito cewa, kamfanin, zai sayar da kowacde daya, kan farashi daga dala 1,600 zuwa dala 2,000 ,inda masu sayen za su tura kudaden zuwa cikin wani Asusun kamfanin da ke a kasar Amurka.
Ya kara da cewa, wannan harkallar, na ci gaba da diga alamar tambaya, ta rashin bin ka’idojin hukumar Kwastam, kan shigo da irin wadannan Kwantaina da kamfanoni na kasar waje ke yi, zuwa cikin kasar nan.
” A bisa tsarin yarjejeniyar wucin gadi ta shigo da Kwantaina cikin kasar nan tare cire masu shinge, za a iya kara shigo da su ne kawai idan an yi amfani da su, gabanin a hukumance a fara sayar da su a cikin kasar, wanda kuma hakan, zai iya kasancewa, bayan hukumar Kwastam, ta tantance su da tsarin biyan kudade fito da kuma na biyan haraji, kan kayan, “A cewarsa.
” Duk wata hada-hadar da aka yi, ba tare da bin wadannan ka’idojin ba, tamkar take hukumarKwastam ta shekarar 2023 ne, musamman duba da cewa, shigo da su ba bisa ka’ida ba, na janyo zurarewa samar da kudaden shiga, da ya kamata Gwamnatin Tarayya ta samu,’ Inji shi.
Ya ci gaba da cewa, hakan janyowa Gwamnatin Tarayya, asarar samun kudaden shiga na fito da suka kai daga dala 350 zuwa dala 400 da kuma kudaden haraji a duk Kwantaina daya.
Ya yi nuni da cewa, bisa rashin samar da kwakyawan tsari a kasar nan a hada-hadar kasuwanci, hakan na kara mayar da kasar, jujin jibge irin wadannan Kwantaina.
Kazalika, ya yi nuni da cewa, hakan zai kuma haifar da cikas, ga kokarin da Babban Bankin Nijeriya ke ci gaba da yi na kara karfafa darajar Naira a kasar nan musamman domin a rage dogaro kan kudaden musaya na kasar waje.
Ya bayyana cewa, ya kamata shugaban hukumar Kwastam na kasar, ya gaggauta dakatar da ci gaba da sayar da Kwantaina na wucin gadi tare da gudanar da cikakken bincike.
Ya bayyana cewa daukar matakai sune kawai mafita kan wannan matsalar, musamman domin a dakile yadda kudaden shiga na Gwamnatin Tarayya ke zurarewa zuwa wata hanya.














Discussion about this post