ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

by Abubakar Abba
45 minutes ago
Jujin

Ana ci gaba yin suka, kan yadda wasu kamfanonin ketare da ke shigo da Kwantaina da babu wasu kaya a cikinsu zuwa cikin kasar, wadanda  kuma ake jibgesu, a duk inda suka ka dama.

Wannan batun wanda a yanzu,  wasu kwararru a fannin sun fara  kira ga mahukunta a kasar, da sanya a fara gudanar da binciken kan jibge Kwantainar, ba bisa bin ka’ida da kamfanobin suka shafr shekaru suna yi, hakan ya sanya hukumar Kustam rasa samun kudaden shiga da suka kai yawan dala miliyan 600.

Wasu daga cikin kwararru a fannin hahada-hadar sufurin Jiragen Ruwa a kasar nan ne, suka bayyana hakan.

ADVERTISEMENT

Daya daga cikinsu, Mista Okey Ibeke,  ya yi kira ga hukumar Kwastam ta kasa  da ta binciki yadda ake shigowa da Kwantainar daga waje tare da kuma sayar da su a cikin kasar nan.

Ibeke wanda ya bayyana haka a taron manema labarai a jihar Legas, ya yi gargadi da cewa, lamarin na janyowa hukumar rashin samun kudaden shiga.

LABARAI MASU NASABA

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Ya buga misali da wasu rahotannin da ke nuna cewa, daya daga cikin irin wadannan kamfanonin da ke aikinsu a cikin kasar, na shirin fara saayar da wasu Kwantaina guda  2,500 da babu wasu kaya a cikinsu a kasar nan.

A cewarsa, an ruwaito cewa, kamfanin, zai sayar da kowacde daya, kan farashi daga dala 1,600 zuwa dala 2,000 ,inda masu sayen za su tura kudaden zuwa cikin wani Asusun kamfanin da ke a kasar Amurka.

Ya kara da cewa, wannan harkallar, na ci gaba da diga alamar tambaya, ta rashin bin ka’idojin hukumar Kwastam, kan shigo da irin wadannan Kwantaina da kamfanoni na kasar waje ke yi, zuwa cikin kasar nan.

” A bisa tsarin yarjejeniyar wucin gadi ta shigo da Kwantaina cikin kasar nan tare cire masu shinge, za a iya kara shigo da su ne kawai idan an yi amfani da su, gabanin a hukumance a fara sayar da su a cikin kasar, wanda kuma hakan, zai iya kasancewa, bayan hukumar Kwastam, ta tantance su da tsarin biyan kudade fito da kuma na biyan haraji, kan kayan, “A cewarsa.

” Duk wata hada-hadar da aka yi, ba tare da bin wadannan ka’idojin ba, tamkar take hukumarKwastam ta shekarar 2023 ne, musamman duba da cewa, shigo da su ba bisa ka’ida ba, na janyo zurarewa samar da kudaden shiga, da ya kamata Gwamnatin Tarayya ta samu,’ Inji shi.

Ya ci gaba da cewa, hakan janyowa Gwamnatin Tarayya, asarar samun kudaden shiga na fito da suka kai daga dala 350 zuwa dala 400  da kuma kudaden haraji a duk Kwantaina daya.

Ya yi nuni da cewa, bisa rashin samar da kwakyawan tsari a kasar nan a hada-hadar kasuwanci, hakan na kara mayar da kasar, jujin jibge irin wadannan Kwantaina.

Kazalika, ya yi nuni da cewa, hakan zai kuma haifar da cikas, ga kokarin da Babban Bankin Nijeriya ke ci gaba da yi na kara karfafa darajar Naira a kasar nan musamman domin a rage dogaro kan kudaden musaya na kasar waje.

Ya bayyana cewa, ya kamata shugaban hukumar Kwastam na kasar, ya gaggauta dakatar da ci gaba da sayar da Kwantaina na wucin gadi tare da gudanar da cikakken bincike.

Ya bayyana cewa daukar matakai sune kawai mafita kan wannan matsalar, musamman domin a dakile yadda kudaden shiga na Gwamnatin Tarayya ke zurarewa zuwa wata hanya.

Jujin
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho
Tattalin Arziki

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000
Tattalin Arziki

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
Tattalin Arziki

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

May 29, 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

June 5, 2026
Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.