… ci gaba daga makon da ya gabata.
Shehu Tijani (RA) ya fada cewa, Faila zata zo, kuma duk an tabbatar, Shehu Ibrahim Inyass Kaulakh yake nufi.
Har ila yau, Shehu Usman dan Fodio (RA) a cikin wakokin sa na fulatanci, a littafin sa na Kanzul Auladi Wazzarari, har sunan Shehu Ibrahim Inyass Kaulakh ya fada, da cewarsa, “wa raida Ibrahimu Sharafuddeen,” ma’ana “bayan mu kuma, akwai Ibrahim Sharafuddeen wanda addini zai daukaka a zamanin sa”, kuma shi ne “Usamuddeen”. Mun gode wa Allah, jikokin sa manya tun daga sarkin musulmi Abubakar na III wadanda suka yi zamani da shehu Ibrahim Inyass Kaulakh har ya zuwa ‘ya’yansa na yanzu, duk sun tabbatar da cewa wannan abu da kakansu ya fada, ilimin shehu Ibrahim Kaulakh yake nufi.
- Majalisar Dattawa Ta Kai Ta’aziyya Ga Al’ummar Kurmin Wali, Ta Yi Alkawarin Kayan Agaji
- Akpabio: Ba A Canza Komai A Cikin Sabbin Dokokin Haraji Ba
To wannan haka waliyan, haka kasar Mali, haka shehu Umar Karaki – wali ne a Ghana da akayi, akwai gidan TB da aka sanya mata suna Umar Karaki TB, sabida kasaitarsa, shi ma ya fadi zuwan Shehu Ibrahim Kaulakh.
Mun gode wa Allah, wannan Shehun namu, Sahibul Faidati, yazo mana da wayewa da komai. Shi ya fara aiki da kayan turawan mulkin mallaka a addinin nan bayan tafiyar su. Wani abun mamaki, Shehu Ibrahim Kaulakh, akan yasa ayi karatu a cikin rediyo, sai da aka ce masa Kafuri a kasar nan tamu Nijeriya, sabida yace dole a saka karatun Alkur’ani a gidan rediyo, a lokacin da aka kafa sabon gidan rediyo na Jaji da ke Kaduna.
Shehu Ibrahim ya fara wa’azi a cikin rediyo a Gambia, inda ya ke cewa a Diwaninsa, “wa lam tura mau’izatun tura’u, min kablihi yanshuruhul mizya’u – ba a taba ganin wa’azi, rediyo tana yadawa ba sai zamanin shehu Ibrahim”.
Wadansu suka ce, “mun gode wa Allah, Allah ya bamu wayayyen malami wanda ya nuna mana lallai mu yi amfani da kayan zamani”, wadansu kuma suka ce, “Riya kenan, a rasa inda za a je a yi wa’azin sai a gidan rediyo”, yanzu wanda ya ce riya ne, da zai zo wannan lokacin a ina ake wa’azin?
Shehu, shi ya nuna mana cewa, in kana da karatu, kuma baka fahimci zamaninka ba, rikici ya faru!
Shehu Ibrahim (RA), shi ya dauke Malamanmu daga reshe (furu’a) da ake cewa su tsaya a kai kawai. Mu malikawa ne, kuma a malikawanma sai malikancin dan Kasim wanda shi ne shehun mu na Afirka, shi ya kawo mana karatun Imam Malik zuwa Misra, don haka, za ka ga littafanmu na malikanci, na Misra ne, Iziyya da su Ishimawi duka ruwayoyi ne na Misra, sabida dan Kasim nan ya dawo. Almajiran Imam Malik suna da yawa, don haka sun dauko karatu kala-kala daga wurinsa, amma muce ba ruwan mu da karatun sai na dan Kasim dinnan, har a cikin mazhabar ma mun takura kanmu a wani waje guda, sannan Imam Malik ba shi kadai ne shugaba a cikin masu mazhaba ba: akwai Shafi’i, da Ahmadu bin Hambal, kuma dukkan su ahlus sunna ne, muce ba ruwan mu da duk karatun su ko da ga hujja tabbatacciya, muce sai Malikanci, to Shehu Ibrahim Kaulakh, shi ya tashi, yace, a’a, mu rika komawa center ta farko Alkur’ani, sannan mabiyinta, ingantacciyar sunnar manzon Allah SAW wacce bata yi karo da Kur’anin nan ba, sabida ba karo tsakanin Allah da manzon Allah SAW, sannan maganganun malamai da ba su yi karo da maganar Allah da manzon Allah ba. “A nasbu kilafun baina daha wa gairihi, ya rahu labibun gairi aini ama’i, – yanzu kace manzon Allah SAW yace kaza, amman kuma malam wane yace kaza, sai nace baka da hankali ne? Za ka hada Annabi SAW da maganar wani Malami, waye Allah ya aiko ma? To, Shehu Ibrahim Kaulakh, shi ya hori shehunnan mu da bin wannan ka’ida, sun sha wuya, musamman a wurin Sallar Kablu.
Mun gode wa Allah, ilimin tarihi na hakeken kasa (archeology) ya fahimtar da kowa ma yanzun, an tono hotuna da irin fasaha ta mutanen da, da annabawansu da Alkur’ani ya bamu labari wajen shekara dubu dari uku kafin haihuwar Annabi Isa (AS). an gano yadda suke Ibada da yadda suka sa hannu akan wani abun mamaki, duk Kur’ani ya gaya mana wannan abun.
Ba don Allah ne ya fada wannan ba, mutane ba za su yarda ba. To mun gode wa Allah.
Ba don kuri ba, wayewa da fahimtar addini cikin sauki, babu kamar almajiran Shehu Ibrahim Inyass Kaulakh. to wanda Allah ya basu wannan Shehi wayayye, dole su godewa Allah. Duk ‘yan adam suna murnar haihuwar wani da ya kawo musu cigaba a addini ko a rayuwa ko a siyasa ko a wayewa.
Mun gode Allah, da ya nuna mana wannan shekara mai alkhairai da yawa. Shekarar da Annabi SAW ya cika shekara 1,500 da haihuwa, duk al’umma suke murna akan haka da kuma zagayowar Maulidin maulanmu Sheikh Ibrahim Kaulakh a watan Rajab, wanda za a yi babban taro a babban gari, garin ilimi, garin sufanci, garin darikar Tijjaniyya, kuma garin Faila na manyan almajiran Sheikh Ibrahim Kaulakha.
Makasudin wannan Maulidi, shi ne godiyan Allah da Allah ya bamu Sheikh Ibrahim Kaulaha, ma’abocin failar Sheikh Tijjani Abul Abbasi wanda alkhairinsa ya game duk musulmi, ba sai sufaye kadai ba, ya game duk sufaye ba sai mu tijjanawa ba, duk masu addini, sun amfanu da albarkar Sheikh Ibrahim Inyass (RA). Sabida ta hanyarsa sufanci ya shiga ofisoshi, ya shiga hatta Saudiyya lokacin da tana kan tashan wahabiyanci.
Amma Allah tabaraka wa ta’ala ya sahhale musu Sheikh Ibrahim, Allah ya sahalewa Sheikh Ibrahim su, sarakunan nasu da komai dole sai da suka yarda da sufanci hatta muftin Saudiyya na wannan lokaci, Ali Sheikh, akwai hotonsa da Shehu yana nan ba daya ba ba biyu ba. To wannan muftin na Saudiyya, wani zance ya shiga tsakaninsa da Shehu Ibrahim Inyass, yake cewa Shehu, “mun gode Allah da muka ganka, yanzu mu ba sai mun sha wahalar zuwa Afrika don fitar da su akan kafurcin da suke yi na sufanci ba, kai dai kowa ya ganka, kowa ya jika ya san malami ne. To yanzu duk abin da kake so, ka bayyana, muna so mu dau nauyin ka da komai, kaje ka fitar da Afrika daga kafurcin da suke yi na darikokin sufaye balle Darikar Tijjaniyya”.
Daga nan, sai Shehu Ibrahim Inyass (RA) ya ce masa, me cece Darikar Tijjaniyya? Sai yace wallahi ban santa ba amma dai na san kafurci ce. Sai yace waye Shehu Tijjani? Me Darikar? Sai yace ban san shi ba amma dai na san batacce ne wanda ya kafa bata. Sai Shehu Ibrahim Inyass yace masa, waye za a tambaya? Wanda ya sani ko wanda bai sani ba? Mufti ya ce, a Ilimance, wanda ya sani shi za a tambaya, sai Shehu (RA) ya ce, to ka ganni nan, na san Darikar Tijjaniyya da kyau, akanta aka haife ni, akanta nake, Mahaifina yana daga cikin mukaddamai manya a cikinta a Senegal kuma a Afrika duk gabaki daya. Sannan na san waye Shehu Tijjani, sharifi ne tun yana dan shekara bakwai ya haddace Kur’ani ya yi kaza ya yi kaza kuma Darikar Tijjaniyya: istigfari ce, da salatin Annabi, da kaza, da kaza.
Shehu ya fadi wannan hikayar ba a wuri daya ba, ba wuri biyu ba, har a hudubar Murtaniya.
Shehu ya ci gaba da yi wa Mufti tambayoyi, har zuwa inda ya ce masa, yanzu musulmi zai wa dan uwansa musulmi huduba cewa, ya bar istigfari ya bar salatin Annabi, yace a’a ba zai yiwu haka ba, sai Shehu yace wannan itace Darikar Tijjaniyya. Sai yace to ai mu ba haka aka gaya mana ba. To yi min littafi, ya gaya Sheikh Ibrahim, imin littafi ka gaya min me cece Darikar Tijjaniyya kuma waye Shehu Tijjani? Don na san ta. Sai Shehu yayi littafin Albayanu wattabiyin, fit Tijjaniyati wat Tijjaniyyina. Wannan littafi muftin Saudiyya ne yasa Shehu Ibrahim ya yi masa. Shehu Ibrahim ya yi wannan irin littafi a ilimance, a wayewa kuma a sufance.
To bayan addu’a Allah ya kawo mana sauran baki mahalarta wannan Maulidi lafiya, Allah yasa a yi taro lafiya kowa ya koma lafiya, Allah ya bai wa kasarmu lafiya, musamman arewacin Nijeriya, Allah ya bamu lafiya da bunkasar arziki, albarkar manzon Allah SAW.
Muna rokon ubangiji ya yi riko da hannun shuwagabannin mu a cikin abin da kasa za ta cigaba, da ‘yan kasa za su cigaba.
Muna kira da duk ‘yan uwanmu musulmi, musamman mabiyan Shehu Ibrahim da muka taru, mu rika koyi da halin Shehu Ibrahim Inyass Kaulakh ta hanyar wayewarsa, kwarewarsa cikin addini, rahamarsa, tausayin (RA) da karantarwarsa da fahimtar sa da zamanin sa.















Discussion about this post