ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asusun NADF Ya Tallafa Wa Manoman Albasa 2,000 A Wasu Jihohin Kasar Nan

by Leadership Hausa
6 months ago

Asusun tallafa wa ci gaban noma na kasa (NADF), ya kaddamar da aikin raba wa manoman Albasa kayan aikin gaggawa.

Kimanin manoman Albasar 2,000 da ke Jihohin Arewacin kasar nan ne, suka amfana da kayan. Asusun ya tallafa musu ne da nufin rage musu radadin ambaliyar ruwan sama da ta lalata gonakinsu a shekarar 2024.

  • Rahoton KPMG Ya Shaida Karfin Gwiwar Kamfanonin Kasa Da Kasa Game Da Bunkasar Tattalin Arzikin Sin A 2026
  • Sheikh Al-Sudais Ya Gargadi Masu Ibadah Kan Kiyaye Darajar Masallatan Harami

Har ila yau, ta gudanar da wannan tallafin ne, bisa hadaka da Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci ta Tarayya. kazalika, an bayar da daukin ne a Jihohin Borno, Yobe, Sakkwato da kuma Kebbi, inda wannan talllafin ya zo daidai da matsayin bangare na kokarin karfafa aiwatar da ajandar ‘Renew Hopes’ ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu, na tallafa wa manoma.

ADVERTISEMENT

Jaridar BusinessDay ta ruwaito cewa, an tallafa kowane manomin an Albasa da buhunhuna hudu na takin zamani, mai nauyin kilo 50, samfurin 15-15 NPK da kuma Irin Albasa da magungunan feshi da na kashe kwari.

Daukacin gwamnonin da ke wadannan jihohin hudu da manoman na Albasa suka amfana da tallafin, sun gode wa asusun na NADF. Sun kuma yi alkawarin ci gaba da yin hadaka da gwamnatin tarayya da sauran masu ruwa da tsaki, musamman a bangaren yin noman Albasa, domin samun riba da kara habaka tattalin aziki da samar da ayyukan yi da kuma rage talauci.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Kazalika, an kaddamar da rabon kayan ne a harabar kamfanin sarrafa takin zamani da ke babban birnin Maiduguri, wanda mallakin Gwamnatin Jihar Borno ne. Babban Sakatare kuma jami’in a Asusun na NADF, Mohammed Ibrahim ya bayyana cewa; wannan tallafin gwamnatin tarayya ce ta samar da shi, bisa nufin rage wa manoman na Albasar a wadannan jihohin asarar da suka yi, sakamakon ambaliyar ruwan sama a kakar noma ta bara da kuma nufin kara bunkasa fannin aikin noma a kasar nan.

Ibrahim, wanda wani jami’i ya wakilce shi a wajen taron rabar da kayan, Shettima Gambo Lawan, ya sanar da cewa; asarar da manoman Albasar suka yi, wani babban kalubale ne da zai iya haifar da koma baya ga fannin na nomanta a kasar da kuma shafar ribar da ya kamata su samu daga fannin, inda ya yi nuni da cewa; wannan tallafi ya zo a kan lokaci.

Ya kara da cewa, wannan tallafi shi ne wanda aka fara gudanarwa a zangon farko, karkashin shirin na asusun NADF, musamman ga manoman da suka yi asara sakamakon iftila’in ambaliyar ruwan sama da kuma na kalubalen sauyin yanayi.

“Manoman Albasa sama da 2,000 ne suka amfana kai tsaye da wannan tallafi, musamman duba da cewa; fannin na noman Albasar a fadin kasar nan, ya kasance yana inganta rayuwar manoman da suka rungumi fannin,” in ji Sakataren.

Ya ci gaba da cewa, sai dai abin takaici; manoman Albasar da dama sun tabka asara biyo bayan samun ambaliyar ruwan saman, musamman a Jihohin Sakkwato, Kebbi, Yobe da kuma Borno. A cewarsa, wannan asarar da suka yi, ta shafi kudaden shigarsu da kuma haifar da karancin Albasar a kasuwanin kasar nan. “Saboda hakan ne, asusun na NADF, ya yi wannan hadaka da gwamonin wadannan jihohi da kuma sauran masu ruwa da tsaki a fannin aikin noma, domin bayar da wannan dauki na gaggawa ga manoman na Albasa da ke fadin wadannan jihohi da nufin kara karfafa wa manoman gwiwa,” a cewarsa.

“Wannan dauki da aka gudanar a yau, an yi shi ne karkashin shirin aiwatar da ajandar ‘Renew Hopes’, na Shugaba Bola Ahmed Tinubu, domin tallafa wa manoma”, a cewar Ibrahim.

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum ne ya kaddamar da rabar da kayan. Babagana, wanda kwamishinan ma’aikatar aikin gona da kula da albarkatun kasa na jihar, Bawu Musawu Alhaji ne, ya wakilce shi a wajen taron tare da yaba wa gwamnatin tarayya kan samar da wannan tallafi.

Ya sanar da cewa, manoman Albasa a jihar 450 ne, suka amfana da wannan tallafi, inda kuma sauran manoma 1,550, da aka zabo a sauran jihohin, suka amfana da wannan tallafi a yayin ambaliyar ruwan sama da ta afku a gonakinsu, a 2024. “A madadin Gwamnatin Jihar Borno da kuma takwarorina, na Yobe, Sakkwato da kuma Kebbi, muna mika godiyarmu ga asusun NADF, kan nuna tausayawarsa na bayar da wannan tallafi,” a cewar Zulum.

“Wannan shirin, ya a nuna a zahiri irin shugabanci na gari da sauraron koken manoma da kuma yin dubi, kan irin gudunmawar da fannin aikin noma ke bayarwa a kasar nan,” in ji gwamnan.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
An Yi Matukar Inganta Harkokin Sadarwa A Kasar Sin Cikin Shekaru Biyar Da Suka Wuce

An Yi Matukar Inganta Harkokin Sadarwa A Kasar Sin Cikin Shekaru Biyar Da Suka Wuce

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.