Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing
Mataimakin firaministan Sin Liu Guozhong, ya yi rangadi a birnin Beijing a yau Lahadi, inda ya jaddada wajibcin nazari da...
Mataimakin firaministan Sin Liu Guozhong, ya yi rangadi a birnin Beijing a yau Lahadi, inda ya jaddada wajibcin nazari da...
Yau ce ranar kandagarkin guguwar rairayi ta duniya, kuma taken ranar a bana shi ne "kare halittu da gonaki daga...
A kwanan nan, ma'aikatar kula da rayuwar jama'a ta kasar Sin ta mika sanarwa ga hukumomin kasar masu inganta rayuwar...
An kashe wani fitaccen kwamandan ’yan bindiga mai suna Kachalla Sani Yellow yayin wani musayar wuta da jami’an tsaro a...
Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC, ta tsawaita wa’adin da ta bai wa jam’iyyun siyasa domin miƙa sunayen...
Shugabar babban taron Majalisar Dinkin Duniya (MDD) na 80, Annalena Baerbock, a kwanan nan ta shaida wa wakiliyar CMG cewa...
Mataimakin zaunannen wakilin Sin dake MDD Sun Lei ya yi jawabi a gun taron kwamitin sulhun MDD kan batun nukiliya...
Li Shulei, babban jami'i a jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin (JKS) ya bayyana cewa, yin nazari sosai a game da...
Xi Jinping, babban sakataren kwamitin tsakiya na jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin kuma shugaban kasar Sin, da Kim Jong Un, babban sakataren jam'iyyar ma'aikata ta Koriya ta Arewa (WPK) kuma shugaban kasar jamhuriyar dimokuradiyyar jama'ar Koriya (DPRK), sun yi musayar gaisuwar taya murna kan cika shekaru 65 da rattaba hannu kan yarjejeniyar abota, hadin gwiwa da taimakon juna tsakanin Sin da DPRK, a yau Asabar. Yayin da duniya ke fuskantar manyan sauye-sauye da ba a taba gani ba cikin karni guda da ya gabata, Xi ya bayyana aniyar yin aiki tare da Kim don kara karfafa tuntubar juna bisa manyan tsare-tsare, da ci gaba da dora huldar Sin da Koriya ta Arewa a kan turba mai kyau, da kuma jagorantar hadin gwiwa mai kyau tsakanin kasashen biyu don samar da karin alfanu ga al'ummomin kasashen biyu, ta yadda za a ba da gudummawa mai kyau wajen karfafa zaman lafiya da ci gaban yanki. A nasa bangaren, Kim ya ce dangantakar abokantaka da hadin gwiwa tsakanin DPRK da Sin, zabi ne mai muhimmanci kuma wata dukiya mai tsada ta jam'iyyunsu biyu da al'ummominsu biyu. Ya ce, zurfafa huldar abokantaka da hadin gwiwa ta tun filazal tsakanin DPRK da Sin kyakkyawan matsayi ne da WPK da gwamnatin DPRK suka dauka, tare da muhimmanta tsarin gurguzu a cikin huldar, don ci gaba da tafiya daidai da irin sauye-sauyen zamani da burin al'ummomin biyu da kuma samun ci gaba mai karfi a dukkan fannoni. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ƙaddamar da rabon buhunan taki 72,000 kyauta tare da magungunan kashe ciyawa da sauran...
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.