Yamal Ya Shana Bayan Barcelona Ta Zazzagawa Valencia Ƙwallo 5 A Raga
Lamine Yamal ya zura kwallaye biyu yayin da Barcelona ta lallasa Valencia da ci 5–0 a ranar Lahadi, inda ta...
Lamine Yamal ya zura kwallaye biyu yayin da Barcelona ta lallasa Valencia da ci 5–0 a ranar Lahadi, inda ta...
Dakarun sojojin sama na kasar Sin, za su halarci bikin nune-nunen jiragen sama na kasa da kasa wanda zai gudana a kasar Masar. Wata sanarwa da rundunar ‘yantar da al’umma ta kasar Sin ko PLA ta fitar a yau Lahadi, ta ce za a aike da nau’o’in jiragen sama daban daban, wajen bikin nune-nunen da za a yi tun daga ranar Talata 8 zuwa Alhamis 10 ga watan nan na Satumba. Sanarwar ta kara da cewa, cikin jiragen da za a tura har da na yaki, da masu gabatar da gargadin gaggawa, da masu karawa jirage mai a sararin sama, da kuma masu saukar ungulu. Wannan ne karo na biyu da za a gudanar da wannan bikin nune-nunen jiragen sama, a filin jirgin saman kasa da kasa na El Alamein, bayan gudanar irinsa na farko a shekarar 2024. A yayin bikin nune-nunen na farko ma jiragen sojin saman kasar Sin sun shiga an dama da su, inda jiragen yaki samfurin J-10, da wani jirgin samfurin Y-20, babban jirgin dakon kayayyaki mafi girma kirar kasar Sin suka gudanar da atisaye. A bana ake cika shekaru 70 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Masar, kuma sassan biyu sun gudanar da jerin ayyukan musaya tsakanin kasashen biyu. A watan da ya gabata, rundunonin sojin saman kasashen biyu, sun kaddamar da jerin atisaye bisa taken "Eagles of Civilization-2026" a kasar Masar. (Saminu Alhassan)
An kaddamar da matsayar hada karfi da karfe, wajen samar da ci gaban bai daya, yayin dandalin kafofin watsa labarai...
Kungiyar ‘Yan Asalin Jihar Kebbi Mazauna Abuja, wato ‘Association Of Kebbi State Indiginous Residents In Abuja’, (AKIRA) ta kaddamar da...
Da safiyar yau Lahadi ne jirgin kasa mai matukar sauri, mai lamba G3998, ya tashi daga tashar Ruijin zuwa birnin...
A gundumar Gyirong ta birnin Xigaze a jihar Xizang mai cin gashin kanta ta kasar Sin, inda ibtila’in zaftarewar kasa...
An bude taron dandalin manyan jami’an kafafen watsa labarai na yankin Asiya da Pacific a yau 5 ga watan nan...
Daren jiya Jumma’a, tawagar likitocin kasar Sin ta 32 da aka kafa bisa jagorancin asibitin Tongren na Beijing da ke...
Mataimakin firaministan kasar Sin, Ding Xuexiang, ya bayyana a jiya Jumma’a cewa, kasar a shirye take ta yi aiki tare...
A kwanan nan, wakilin kafar CMG ya yi hira da Sodiq Safoev, babban mataimakin shugaban majalisar dattawa ta kasar Uzbekistan,...
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.