ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Matakin Da Muka Dauka Kan Murabus Din Okupe – Kwamitin Yakin Zaben Peter Obi

by Sadiq
4 years ago
Okupe

Kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party, ya ce har yanzu bai yanke shawara kan matakin da babban daraktanta, Doyin Okupe ya dauka na yin murabus daga mukaminsa ba.

Okupe dai ya mika takardar murabus dinsa ga dan takarar jam’iyyar, Peter Obi biyo bayan hukuncin da aka yanke masa a gaban kotu kan karya dokar halatta kudaden haram.

  • Yadda Zan Inganta Rayuwar Talakawan Gombe- Mailantarki Na NNPP
  • Za A Fara Rijistar Shiga Makarantun Gaba Da Sakandire UTME 14 Ga Janairun 2023 —JAMB

Idan ba a manta ba a ranar Litinin ne wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta yanke wa Okupe hukuncin daurin shekaru biyu a gidan yari kan laifin karkatar da kudi.

ADVERTISEMENT

Shugaban kamfen din ya fada a ranar Talata cikin wasikar murabus dinsa cewa lokaci ya yi da ya kamata ya ajiye mukaminsa amma ya ce goyon bayansa ga Obi har ya kai ga nasara a 2023.

Sai dai babban mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben, Tanko Yunusa a wata hira da gidan talabijin na Channels, ya ce kwamitin zai gana kafin ya yi wani bayani kan murabus din Okupe.

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

A cewarsa, mutum ba zai iya daukar irin wannan matakin ba yana mai dagewa cewa kwamitin zai yi taro ya dauki matakin gamayya wanda zai zama maslaha ga dukkan ‘yan Nijeriya.

Ya ce, “Ba mu fitar da wata sanarwa a hukumance dangane da murabus din Dakta Doyin Okupe ba har sai kwamitin yakin neman zaben ya yi taro ya yanke shawarar abin da za a yi da kuma yadda za a yi.

“Don haka wadannan labaran na iya zama hasashe har sai kwamitin kamfen ya yi taro. Mu ba mutane masu zaman kansu ba ne inda mutum daya zai iya yanke hukunci Za a yanke shawara ne domin maslahar al’ummar Nijeriya”.

MASU ALAKA

Okupe
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa
Manyan Labarai

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026
Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000  A Kaduna
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

July 26, 2026
Next Post
Abokan Hamayyata Ba Su Da Nagarta – Tinubu

Abokan Hamayyata Ba Su Da Nagarta - Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Okupe

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Okupe

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Okupe

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.