Ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya tabbatar wa magoya bayansa cewa babu wanda zai sake tsoratar da su ko ya hana a ƙirga kuri’unsu a zaɓen shekarar 2027.
Obi ya bayyana hakan ne a wani taron tattaunawa da masu kaɗa ƙuri’a a Fatakwal, Jihar Rivers, inda ya ce jam’iyyarsa za ta tabbatar da samun isasshen tsari da haɗin kai a rumfunan zaɓe domin daƙile duk wani yunƙurin tsoratar da masu kaɗa ƙuri’a.
Ya ce yawan jami’an da ake samu a rumfar zaɓe ba zai tsoratar da ɗimbin masu kaɗa ƙuri’a ba, yana mai cewa dole ne ‘yan Nijeriya su tsaya tsayin daka wajen kare haƙƙinsu na zaɓe.
A nasa ɓangaren, mataimakinsa a takarar, Rabiu Kwankwaso, ya gargaɗi jam’iyyun siyasa da kada su dogara da yawan gwamnonin da suke da su a matsayin tabbacin samun nasara a zaben 2027.
Obi ya kuma jaddada cewa manufarsu ita ce tabbatar da cewa ƙuri’ar kowane ɗan Nijeriya an ƙirga ta, yana mai kira ga magoya bayansa da su kasance cikin shiri domin kare zaɓinsu a lokacin zaɓe.














