ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bam Ya Kashe Matasa 4 A Garin Banki

by Abubakar Sulaiman
7 months ago
Matasa

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Wani Bam da ya fashe a garin Banki na ƙaramar hukumar Bama a Jihar Borno, inda wani abin fashewa da aka ƙera a gida (IED) ya tarwatse wanda yayi sanadiyar kashe matasa huɗu. Lamarin ya faru ne a bayan tashar motar Banki a unguwar Wajari, kamar yadda rundunar ƴansanda ta tabbatar. Matasan sun gamu da ajalinsu ne yayin da suke wasa da kayan da suka tsinta a daji, wanda daga bisani ya fashe.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya ce sun samu  rahoto daga wani mazaunin yankin da misalin karfe 1 na rana, abin da ya sa DPO da tawagarsa tare da kwararru kan kwance Bam (EOD) suka hanzarta zuwa wurin. Sun keɓe yankin domin bincike, tare da tabbatar da mutuwar matasa hudu, yayin da wani yaro mai shekaru 12, Mustapha Tijja, ya tsira amma ya samu munanan raunuka. An garzaya da shi asibitin FHI 360 dake Banki, inda yake karɓar magani.

  • Borno Ta Kashe Naira Biliyan 100 Kan Samar Da Tsaro A 2025 – Gwamna Zulum
  • Bashin Da Bankin AfDB Ya Bai Wa Nijeriya Ya Kai Dala Biliyan 5.1

Binciken farko ya nuna cewa Mustapha da abokansa huɗu sun shiga wani ɗakin da aka gina na wucin gadi a bayan tashar motar, inda marigayin ke wasa da na’urar fashewar da suka ɗauko daga daji. Sai ta fashe har ta kashe Awana Mustapha mai shekaru 15, da Malum Modu 14, da Lawan Ibrahim 12, da kuma Modu Abacha 12. Hukuma ta tabbatar da kwantar hankula da zaman lafiya a yankin, sannan tana ci gaba da gudanar da cikakken bincike.

ADVERTISEMENT

Kwamishinan ƴansanda, CP Naziru Abdulmajid, ya jajanta wa iyalan da abin ya shafa, tare da gargaɗin jama’a musamman yara da su guji taɓa wa ko wasa da duk wani abu da ba su sani ba, musamman waɗanda ake zargin na’urar fashewa ce. Ya buƙaci al’umma da su riƙa kai rahoto nan take idan suka ga wani abu da suke shakku a kowane lokaci.

Matasa
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu
  • Abubakar Sulaiman
    Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano
  • Abubakar Sulaiman
    An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala
Labarai

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON
Labarai

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Next Post
“Lokaci Ya Yi Da Arewa Za Ta Farka Daga Bacci”

“Lokaci Ya Yi Da Arewa Za Ta Farka Daga Bacci”

LABARAI MASU NASABA

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

July 17, 2026
Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.