Wani Bam da ya fashe a garin Banki na ƙaramar hukumar Bama a Jihar Borno, inda wani abin fashewa da aka ƙera a gida (IED) ya tarwatse wanda yayi sanadiyar kashe matasa huɗu. Lamarin ya faru ne a bayan tashar motar Banki a unguwar Wajari, kamar yadda rundunar ƴansanda ta tabbatar. Matasan sun gamu da ajalinsu ne yayin da suke wasa da kayan da suka tsinta a daji, wanda daga bisani ya fashe.
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya ce sun samu rahoto daga wani mazaunin yankin da misalin karfe 1 na rana, abin da ya sa DPO da tawagarsa tare da kwararru kan kwance Bam (EOD) suka hanzarta zuwa wurin. Sun keɓe yankin domin bincike, tare da tabbatar da mutuwar matasa hudu, yayin da wani yaro mai shekaru 12, Mustapha Tijja, ya tsira amma ya samu munanan raunuka. An garzaya da shi asibitin FHI 360 dake Banki, inda yake karɓar magani.
- Borno Ta Kashe Naira Biliyan 100 Kan Samar Da Tsaro A 2025 – Gwamna Zulum
- Bashin Da Bankin AfDB Ya Bai Wa Nijeriya Ya Kai Dala Biliyan 5.1
Binciken farko ya nuna cewa Mustapha da abokansa huɗu sun shiga wani ɗakin da aka gina na wucin gadi a bayan tashar motar, inda marigayin ke wasa da na’urar fashewar da suka ɗauko daga daji. Sai ta fashe har ta kashe Awana Mustapha mai shekaru 15, da Malum Modu 14, da Lawan Ibrahim 12, da kuma Modu Abacha 12. Hukuma ta tabbatar da kwantar hankula da zaman lafiya a yankin, sannan tana ci gaba da gudanar da cikakken bincike.
Kwamishinan ƴansanda, CP Naziru Abdulmajid, ya jajanta wa iyalan da abin ya shafa, tare da gargaɗin jama’a musamman yara da su guji taɓa wa ko wasa da duk wani abu da ba su sani ba, musamman waɗanda ake zargin na’urar fashewa ce. Ya buƙaci al’umma da su riƙa kai rahoto nan take idan suka ga wani abu da suke shakku a kowane lokaci.














