Shugaban ƙungiyar masu sayar da ganye da kayan marmari na Kasuwar Utako Babban Birnin Tarayya Abuja Hamza Mu’azu Karwai yayi kira da Shugabannin ƙungiyar tuntuɓa ta Arewa su ƙara ta shi tsaye wajen kare shi sashen na Arewa daga waɗansu abubuwan cin fuskar da ake yiwa Arewa da su ‘ya’yan nata, Shugaban bai tsaya anan ba saboda kuwa ita ma ƙungiyar dattawan Arewa ya yi kira gare ta, ita ma ai tana da irin tata gudunmawar da za ta riƙa badawa wajen kare muradan shi sashen na Arewa.
Mu’azu ya bayyana hakan ne lokacin daya kiran manema labarai a ofishinsa da ya ke cikin kasuwar ta Utako,ya yi bayanin cewar ba wai kowane lokaci bane za’a tsaya a riƙa yin shiru, amma ga shi ana yi ma ‘ayan Arewa cin kashi, su basu tsira cikin sashen na Arewa ba ballatana ace sun tafi zuwa sashen Kudanci, domi mutanen da suka bar Zariya zuwa ɗaurin aure daga cikin mutum 32 haka aka sa wa motar tasu wuta,a ƙalla mutum 12 an kashe su wasu kuma sun samu raunuka, an kama mutane 22 da ake zargi da aikata laifi amma har yanzu abin shiru kamar an shuka Dussa.
- Ci Gaban Fasahar AI A Kasar Sin Ya Nuna Gazawar Matakan Amurka Na Tare Hanyar Sin
- Ta’addanci: Ko Matakan Shawo Kan Taɓarɓarewar Tsaro Za Su Yi Tasiri?
Ga kuma mutane 16 ƴan asalin Jihar Kano waɗanda suma an kashe su a Jihar Edo akan hanyarsu ta komawa gida Kano daga Fatakwal, suma hakan abin ya tafi kamar an kashe kiyashi,duk da yake ita gwamnatin Jihar Edo ta ce zata biya diyya. Mu’azu ya ce ba zai manta ba da harin da aka kai Tudun Biri inda aka ce Jirgin da mai da matuƙi yayi kuskure hakanan mutane 88 suka mutu wajen 66 sukasamu munanan raunuka, abin ya kasance sau biyu ne duk a rana ɗaya amma abin sai dai ace Allah ya ƙara kare mu.
Ya ce muddin dai za ‘a ci gaba da tafiya cikin irin wannan yanayi na yadda ake nuna kamara bamu da makoma sai da I duk wanda ya ga dama ya ci mana mutunci a ja baki ayi shiru,hakan bai dace a ci gaba da tafiya hakan ba ɗaukar matakin da ya dace haka zai ta ci gaba. Ya ce da ace ‘yan asalin Jihar Edo ne aka kashe a Kano mi ake tsammanin zai faru.?
Ya yi kira da su Shugabannin cewar ba wai ya rena jagorancin da suke ba, amma da akwia buƙatar su sake zage damtse abin yana da matuƙar wuya. Dangane da ritaya Janar Christopher Musa da aka bada sunansa domin ba shi muƙamin Ministan tsaro, ya ce yana yi ma shi tafan alkhairi, daga ƙarshe ya yi kira da Gwamna Jihar Kano ya ci gaba da ɗaukar matakan tsaron da za su kai ga hana ‘yan ta’adda shiga Kano suna garkuwa da mutane tare da kashe su, Allah ya kiyaye yana kuma yi ma shi fatan alkhairi.














