ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Borno Ta Kashe Naira Biliyan 100 Kan Samar Da Tsaro A 2025 – Gwamna Zulum

by Abubakar Sulaiman
7 months ago
Borno

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta kashe kusan Naira biliyan 100 a shekarar 2025 wajen tabbatar da tsaro, lamarin da ya ce ya yi wa ci gaban jihar babban cikas. Ya bayyana haka ne yayin ziyarar sa ga Sarkin Uba, Ali Ibn Mamza, a garin Uba na ƙaramar hukumar Askira/Uba, domin duba halin tsaro a yankin. Gwamnan ya ce matsalolin tsaro sun hana gwamnati aiwatar da muhimman ayyukan raya ƙasa, musamman gine-ginen hanyoyi da ake shirin ƙaddamarwa.

Zulum ya nuna damuwa kan yadda hare-hare ke sa ma’aikata da ƴan kwangiloli barin wuraren aiki, abin da ya daƙile manufofin cigaban jihar. Ya ce wannan ne ya sanya gwamnati ke kafa wurin hakar duwatsu a Gwoza tare da sayen manyan motocin aiki 100 domin hukumar gyaran hanyoyi ta iya bin diddigin shirye-shiryen samar da hanyoyi ba tare da dogaro ga kwangiloli na waje ba. Ya jaddada cewa idan an samu zaman lafiya, adadin kuɗin da ake kashewa kan tsaro za a mayar da su kan harkokin ilimi, da lafiya da sauran muhimman ayyuka.

  • ISWAP Ta Kashe Jami’ai 8 A Wani Sabon Hari A Borno
  • Ƴansanda Sun Fara Tabbatar Da Dokar Hana Zirga-zigar Babura A Kano

Duk da ƙalubalen tsaro, gwamnan ya tabbatar wa jama’ar yankin cewa nan ba da jimawa ba za a fara gudanar da sabbin aiyuka, ciki har da gina hanyoyi, da kafa cibiyoyin kimiyya da kwamfuta da kuma wasu muhimman makarantu a yankin. Ya ce gwamnatin jihar na da shirin tabbatar da cewa al’ummar Borno ba za su rasa sauyin da suke muradi ba duk da matsalolin da ake fuskanta. Ya ƙara da cewa gwamnati tana fito da tsare-tsare na dogon lokaci domin tabbatar da ɗorewar cigaba bayan samun kwanciyar hankali.

ADVERTISEMENT

A nasa ɓangaren, Sarkin Uba, Ali Ibn Mamza, ya yaba wa gwamna Zulum bisa jajircewarsa wajen gudanar da aiyukan raya ƙasa duk da matsalolin tsaro da jihar ke fama da su. Ya ce abubuwan da gwamnati ta yi suna nan a bayyane, yana mai gode wa gwamnan kan kulawa da tallafin da ake bai wa al’ummar Uba. Sarkin ya tabbatar da cewa za su ci gaba da yin addu’o’i domin samun zaman lafiya mai ɗorewa a Borno da ƙasa baki ɗaya.

Borno
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki

MASU ALAKA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Next Post
Za A Gudanar Da Bajakolin Litattafai Da Al’adun Hausa Karo Na 5 A Kaduna

Za A Gudanar Da Bajakolin Litattafai Da Al'adun Hausa Karo Na 5 A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.