ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ban Yarda A Ware Watan Muharram Don Maulidina Ba – Marigayi Sheikh Dahiru Bauchi 

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
6 months ago
Dahiru Bauchi

Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya bayyana cewar bayan ya rasu bai amince ba kuma bai yarda a ware rana ta musamman a ranar 2 ga watan Al-Muharram domin ake yin Mauludin tunawa da ranar haihuwarsa ba.

 

Marigayin ya bayyana haka ne daga cikin wasiyyar da bayar, cikin tawali’u da ƙanƙan da kai ya ce shi bai kai wanda za a ke gudanar da Maulidin tunawa da shi ba kamar yadda ake yi wa Manzon Rahama, irin su Shehu Tijjani da Shehu Ibrahim Inyass.

ADVERTISEMENT
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 25 A Wani Sabon Hari Kan Iyakar Kano
  • Gwamnatin Kano Ta Musanta Jita-jitar Barazanar Tsaro A Jihar

Marigayi wanda ya rasu a ranar Alhamis ya bayyana cewar shi kawai Muƙaddami ne daga cikin Muƙaddaman Shehu, kuma hadiminsa sannan surukinsa inda ya bayyana cewa hakan ma kawai ya ishe sa alfahari.

 

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Shehu Dahiru Bauchi ya nuna cewa, idan har an ce kowani Muƙaddamin Shehu za a ke masa Maulidin tunawa da shi to kowani rana ma zai zama na gudanar da maulidodi ne domin yawan Muƙaddaman da ake da su.

 

Ya bayyana da bakinsa cewa: “Amma ni ban yarda a ce wata rana za a yi taro, yau 2 ga watan Muharram ranar da aka haifi Shehu Dahiru, ita muke yi wa Maulidi, ban yarda ba, kada a yi min bayan rasuwa ta.

 

“Amma na ji wani yana cewa, Rabi’ul Auwal ya kunso mana (ya zo mana) da Annabi Muhammadu (SAW), Safar ya kunso mana Shehu Tijjani (RA), Rajab ya kunso mana Shehu Ibrahim (RA), ya ce wai Muharram ya kunso musu Shehu Dahiru to wannan kada a sake fada, kada na sake ji.

 

“Ni ba kowa ba ne cikin wannan tsarin, ni Muƙaddami ne. Ni Muƙaddami ne daga cikin muƙaddaman Shehu. Yanzu kowani Muƙaddamin Shehu sai an masa Maulidi ranar haihuwarsa nawa kenan? akwai ranar da za ta wuce ba a samu Maulidi ba?

 

“In an ce kowani Muƙaddamin Shehu za a masa Maulidi akwai ranar da ba Maulidi ke nan a Nijeriya? To ban yarda kada a sa sunana a cikin waɗanda ake ma wannan abu,” in ji shi.

 

Ya sake fayyace wasiyyar tasa da cewa, “Kuma ko na mutu kada a ce yau ranar biyu ga watan Muharram za a yi Maulidin Shehu Dahiru, ban yarda ba!, ban yarda ba!!; A bar ni kamar sauran ‘yan uwana Mukaddamai.”

 

Ya sake nanata cewa shi “Ni ba kowa ba ne illa muƙaddami cikin Muƙaddaman Shehu kuma wannan ya isheni alfahari, hadiminsa kuma surukinsa, Alhamdulillahi.”

 

A gefe guda ya ce Maulidin tunawa da Shehu Ibrahim da ake yi a watan Rajab shi ne ya fara gudanarwa.

Dahiru Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba
Dahiru Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Peng Liyuan Ta Halarci Aikin Fadakarwa Albarkacin “Ranar Cutar Sida Ta Duniya” Ta 2025

Peng Liyuan Ta Halarci Aikin Fadakarwa Albarkacin “Ranar Cutar Sida Ta Duniya” Ta 2025

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.