ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bangarorin Da Ke Rikici Da Juna A Sudan Sun Amince Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta

by Sadiq
3 years ago
Sudan

Sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa na musamman da suka shafe kwanaki hudu suna gwabza fada domin samun galaba a kasar, sun amince da tsagaita wuta na tsawon sa’o’i 24.

Tashin hankalin ya kunno kai yayin da fadan da ke ci gaba da yin barazanar jefa kasar cikin rudani.

  • Me Ya Sa Dukkan Jami’an Amurka Ke Tattaunawa Kan Kasar Sin A Argentina?
  • An Kaddamar Da Bikin Haduwar Matasan Sin Da Afirka Karo Na 7

Miliyoyin ‘yan Sudan da ke babban birnin kasar da sauran manyan biranen kasar, sun fake a gidajensu, inda suka shiga cikin tashin hankali yayin da dakarun biyu suka yi ruwan bama-bamai a wuraren da jama’a ke zama da manyan bindigogi da jiragen sama tare da yin luguden wuta a kan titi.

ADVERTISEMENT

A ‘yan kwanakin nan mayakan Khartoum suka kai hari kan ayarin motocin ofishin jakadancin Amurka tare da kutsawa gidan wakilin Tarayyar Turai a Sudan, amma babu wani harin da aka kai kan wani jami’i.

A ranar Litinin ne aka kai wa ayarin motocin ofishin jakadancin Amurka hari, kuma rahotannin farko na alakanta maharan da dakarun Rapid Support Forces, kungiyar sa-kai da ke yaki da sojojin Sudan, kamar yadda majiyar ta shaida wa sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken.

LABARAI MASU NASABA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

Ya kara da cewa dukkan mambobin ayarin na cikin koshin lafiya.

Rahotanni sun ruwaito Laftanar Janar Shams El Din Kabbashi, babban kwamandan dakarun kai daukin gaggawa na musamman, yana cewa sojojin za su mutunta yarjejeniyar tsagaita bude wuta, yayin da shugaban rundunar sojin kasar Janar Abdel Fattah Burhan ke cewa dakarunsa za su mutunta yarjejeniyar.

Sai dai dukkanin bangarorin sojin biyu, ba su fito fili su sanar da batun tsagaita wuta nan take ba.

Bayanai sun ce, an sake samun arangama a kusa da hedikwatar sojojin da kuma kusa da filin jirgin sama, wurare biyu masu muhimmanci da ake gwabzawa ke nan yanzu haka, tun bayan barkewar fada a ranar Asabar.

An kuma gwabza fada a kusa da wani muhimmin sansanin sojin sama a Merowe, mai tazarar kilomita 350 daga Arewa Maso Yammacin birnin Khartoum.

Fiye da mutane 185 ne aka kashe yayin da wasu fiye da 1,800 suka jikkata tun bayan barkewar fadan a ranar Asabar, a cewar alkaluman Majalisar Dinkin Duniya.

Sai dai kungiyar likitocin Sudan ta sanar a ranar Talata cewa akalla fararen hula 144 ne aka kashe tare da jikkata wasu fiye da 1,400.

Adadin wadanda suka mutu zai iya zarce haka saboda fadan da aka yi a birnin Khartoum ya hana kwashe gawarwaki a wasu yankuna.

Wannan lamari dai, ya tayar da hankulan jama’a a wani abu da ake ganin yakin basasa ne, dai-dai lokacin da al’ummar Sudan ke kokarin farfado da tsarin mulki na farar hula ta dimokuradiyya, bayan shekaru da dama suna karkashin mulkin soja.

MASU ALAKA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
Kasashen Ketare

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

May 30, 2026
Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Kasashen Ketare

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

May 30, 2026
Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu

May 30, 2026
Next Post
Wasu Yankunan Afirka Na Fuskantar Barazanar Yunwa —MDD

Wasu Yankunan Afirka Na Fuskantar Barazanar Yunwa —MDD

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.