ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bangarorin Da Ke Rikici Da Juna A Sudan Sun Amince Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta

by Sadiq
3 years ago
Sudan

Sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa na musamman da suka shafe kwanaki hudu suna gwabza fada domin samun galaba a kasar, sun amince da tsagaita wuta na tsawon sa’o’i 24.

Tashin hankalin ya kunno kai yayin da fadan da ke ci gaba da yin barazanar jefa kasar cikin rudani.

  • Me Ya Sa Dukkan Jami’an Amurka Ke Tattaunawa Kan Kasar Sin A Argentina?
  • An Kaddamar Da Bikin Haduwar Matasan Sin Da Afirka Karo Na 7

Miliyoyin ‘yan Sudan da ke babban birnin kasar da sauran manyan biranen kasar, sun fake a gidajensu, inda suka shiga cikin tashin hankali yayin da dakarun biyu suka yi ruwan bama-bamai a wuraren da jama’a ke zama da manyan bindigogi da jiragen sama tare da yin luguden wuta a kan titi.

ADVERTISEMENT

A ‘yan kwanakin nan mayakan Khartoum suka kai hari kan ayarin motocin ofishin jakadancin Amurka tare da kutsawa gidan wakilin Tarayyar Turai a Sudan, amma babu wani harin da aka kai kan wani jami’i.

A ranar Litinin ne aka kai wa ayarin motocin ofishin jakadancin Amurka hari, kuma rahotannin farko na alakanta maharan da dakarun Rapid Support Forces, kungiyar sa-kai da ke yaki da sojojin Sudan, kamar yadda majiyar ta shaida wa sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Ya kara da cewa dukkan mambobin ayarin na cikin koshin lafiya.

Rahotanni sun ruwaito Laftanar Janar Shams El Din Kabbashi, babban kwamandan dakarun kai daukin gaggawa na musamman, yana cewa sojojin za su mutunta yarjejeniyar tsagaita bude wuta, yayin da shugaban rundunar sojin kasar Janar Abdel Fattah Burhan ke cewa dakarunsa za su mutunta yarjejeniyar.

Sai dai dukkanin bangarorin sojin biyu, ba su fito fili su sanar da batun tsagaita wuta nan take ba.

Bayanai sun ce, an sake samun arangama a kusa da hedikwatar sojojin da kuma kusa da filin jirgin sama, wurare biyu masu muhimmanci da ake gwabzawa ke nan yanzu haka, tun bayan barkewar fada a ranar Asabar.

An kuma gwabza fada a kusa da wani muhimmin sansanin sojin sama a Merowe, mai tazarar kilomita 350 daga Arewa Maso Yammacin birnin Khartoum.

Fiye da mutane 185 ne aka kashe yayin da wasu fiye da 1,800 suka jikkata tun bayan barkewar fadan a ranar Asabar, a cewar alkaluman Majalisar Dinkin Duniya.

Sai dai kungiyar likitocin Sudan ta sanar a ranar Talata cewa akalla fararen hula 144 ne aka kashe tare da jikkata wasu fiye da 1,400.

Adadin wadanda suka mutu zai iya zarce haka saboda fadan da aka yi a birnin Khartoum ya hana kwashe gawarwaki a wasu yankuna.

Wannan lamari dai, ya tayar da hankulan jama’a a wani abu da ake ganin yakin basasa ne, dai-dai lokacin da al’ummar Sudan ke kokarin farfado da tsarin mulki na farar hula ta dimokuradiyya, bayan shekaru da dama suna karkashin mulkin soja.

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Kasashen Ketare

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
Kasashen Ketare

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026
Next Post
Wasu Yankunan Afirka Na Fuskantar Barazanar Yunwa —MDD

Wasu Yankunan Afirka Na Fuskantar Barazanar Yunwa —MDD

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

July 18, 2026
Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

July 18, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.