ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bangarorin Da Ke Rikici Da Juna A Sudan Sun Amince Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta

by Sadiq
3 years ago
Sudan

Sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa na musamman da suka shafe kwanaki hudu suna gwabza fada domin samun galaba a kasar, sun amince da tsagaita wuta na tsawon sa’o’i 24.

Tashin hankalin ya kunno kai yayin da fadan da ke ci gaba da yin barazanar jefa kasar cikin rudani.

  • Me Ya Sa Dukkan Jami’an Amurka Ke Tattaunawa Kan Kasar Sin A Argentina?
  • An Kaddamar Da Bikin Haduwar Matasan Sin Da Afirka Karo Na 7

Miliyoyin ‘yan Sudan da ke babban birnin kasar da sauran manyan biranen kasar, sun fake a gidajensu, inda suka shiga cikin tashin hankali yayin da dakarun biyu suka yi ruwan bama-bamai a wuraren da jama’a ke zama da manyan bindigogi da jiragen sama tare da yin luguden wuta a kan titi.

ADVERTISEMENT

A ‘yan kwanakin nan mayakan Khartoum suka kai hari kan ayarin motocin ofishin jakadancin Amurka tare da kutsawa gidan wakilin Tarayyar Turai a Sudan, amma babu wani harin da aka kai kan wani jami’i.

A ranar Litinin ne aka kai wa ayarin motocin ofishin jakadancin Amurka hari, kuma rahotannin farko na alakanta maharan da dakarun Rapid Support Forces, kungiyar sa-kai da ke yaki da sojojin Sudan, kamar yadda majiyar ta shaida wa sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken.

LABARAI MASU NASABA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

Ya kara da cewa dukkan mambobin ayarin na cikin koshin lafiya.

Rahotanni sun ruwaito Laftanar Janar Shams El Din Kabbashi, babban kwamandan dakarun kai daukin gaggawa na musamman, yana cewa sojojin za su mutunta yarjejeniyar tsagaita bude wuta, yayin da shugaban rundunar sojin kasar Janar Abdel Fattah Burhan ke cewa dakarunsa za su mutunta yarjejeniyar.

Sai dai dukkanin bangarorin sojin biyu, ba su fito fili su sanar da batun tsagaita wuta nan take ba.

Bayanai sun ce, an sake samun arangama a kusa da hedikwatar sojojin da kuma kusa da filin jirgin sama, wurare biyu masu muhimmanci da ake gwabzawa ke nan yanzu haka, tun bayan barkewar fada a ranar Asabar.

An kuma gwabza fada a kusa da wani muhimmin sansanin sojin sama a Merowe, mai tazarar kilomita 350 daga Arewa Maso Yammacin birnin Khartoum.

Fiye da mutane 185 ne aka kashe yayin da wasu fiye da 1,800 suka jikkata tun bayan barkewar fadan a ranar Asabar, a cewar alkaluman Majalisar Dinkin Duniya.

Sai dai kungiyar likitocin Sudan ta sanar a ranar Talata cewa akalla fararen hula 144 ne aka kashe tare da jikkata wasu fiye da 1,400.

Adadin wadanda suka mutu zai iya zarce haka saboda fadan da aka yi a birnin Khartoum ya hana kwashe gawarwaki a wasu yankuna.

Wannan lamari dai, ya tayar da hankulan jama’a a wani abu da ake ganin yakin basasa ne, dai-dai lokacin da al’ummar Sudan ke kokarin farfado da tsarin mulki na farar hula ta dimokuradiyya, bayan shekaru da dama suna karkashin mulkin soja.

MASU ALAKA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya
Kasashen Ketare

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

June 23, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Kasashen Ketare

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

June 22, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran
Kasashen Ketare

Iran Ta Ce Shirinta Na Makamai Masu Linzami Ba Ya Cikin Tattaunawa Da Amurka

June 18, 2026
Next Post
Wasu Yankunan Afirka Na Fuskantar Barazanar Yunwa —MDD

Wasu Yankunan Afirka Na Fuskantar Barazanar Yunwa —MDD

LABARAI MASU NASABA

Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.