Wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar APC a Kano, ciki har da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau I. Jibrin, da Salihu Sagir Takai, sun bayyana goyon bayansu ga Kabiru Alhassan Rurum a matsayin ɗaya daga cikin fitattun ‘yan takarar kujerar mataimakin gwamna.
Wannan matsaya ta fito ne bayan wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a daren Lahadi, inda aka fitar da sunaye uku domin cike gurbin da ya biyo bayan murabus ɗin Aminu Abdussalam Gwarzo.
- Ban Fuskanci Matsala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Asiya Muhammad
- David Mark Ya Ƙaryata Jita-jitar Murabus, Ya Ce Ƙarya Ce Tsagwaronta
An bayyana cewa an gudanar da taron ne bisa umarnin gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf, wanda ya buƙaci a gabatar masa da sunaye uku domin zaɓen wanda ya dace, tare da jaddada cewa an bi wannan umarni yadda ya kamata duk da jita-jitar da ke yawo.
Sunayen da aka gabatar sun haɗa da Kabiru Alhassan Rurum, da. Rabiu Sulaiman Bichi da kuma Murtala Sule Garo, inda kowannensu ya samu goyon bayan ɓangarori daban-daban na jam’iyyar.
Haka kuma, wasu daga cikin masu ruwa da tsakin sun buƙaci a bai wa yankin Kano ta Kudu dama a wannan muƙami, yayin da jerin sunayen da aka gabatar ke jiran hukuncin ƙarshe daga gwamna Yusuf domin tantancewa da naɗin wanda zai maye gurbin mataimakin gwamnan.















Discussion about this post