Mun dai ƙara dawo, domin yin sharhi, domin wannan Jaridar, ba sau ɗaya ba sau biyu ba, ba kuma sau uku ba, ta yi sharhi kan koma bayan da aka samu a shekarun baya, na rashin iya gudanar da shugabanci na gari, a ƙasar.
Kazalika, a sharhin Jaridar na baya, ta bayyana jeren yawan ƴan Adama da aka kashe a wasu ƙauyuka da kuma yin tir da gazarwar tsare-tsaren da mhukunta suka samar.
Duk a sharhin na baya, Jaridar ta kuma buƙaci da a tabbatar da an wanzar da yin gaskiya.
Bayan kasheshen da ƴan bindiga suka yi a, Kajuru, after Zangon Kataf, da kuma wanda suka yi a Chikun, bayan kisan da suka yi, a ranar bikin Kirsimete, da sauran kashe-kashen rashin imani da suka aiwatar a yankin Arewa maso Yamma, hakan na ci gaba da zama, abin baƙin ciki.
Wannan sharhin Jaridar na yanzu, ya bijoro ne, biyo bayan sake kai wasu sabbin hare-haren da ƴan bindigar suka ƙaddamar a ƙauyen Naridon, na mazaɓar Kamaru, da harin masarautar Chawai, a ƙaramar hukumar Kauru a Kaduna.
Miyagun, sun kai harin ne, a daren ranar, 27 na watan Yulin 2026, inda suka ɗauki rayukan waɗanda ba su ji, kuma basu gani ba har guda talatin, wanɗanda daga cikinsu, akwai maza tara, mata goma sai kuma yara sha ɗaya.
Bugu da ƙari, a ranar ɗaya na watan Agustan 2026, Cocin Catholic Diocese da ke a garin Kafanchan, ta gudanar da bizne mutane 27, da ƴan bindiga suka hallaka.
Ya zuwa yanzu, sau uku ke nan, ana kai hare-hare a cikin dai wannan ƙauyen duk a cikin watanni sha ɗaya.
Mun ƙara bijero da wannan sharhin ne, ba wai domin cewa, irin waɗannan rubuce-rubucen za su iya kawo ƙarshen gazawar da mahukuntan, suka yi a shekaru bay aba, sai domin a sake fargar da su.
Wannan sharhin, ƙunshe yake da hujoji da dama, musamman na irin ƙalubalen rashen tsaro, da Nijeriya ke ci gaba da fuskanta, wanda kuma ya waja, mahukunta su farka daga barcinsu, domin yin wani abu akai.
A cewar wani ganau, mai suna Mark Ɓincent, hare-haren na kwana-kwanan, sun zo ne, a cikin jimamin firgici da tsoratarwa, musamman duba da cewa, an gudanar da su ne, a tsakiyar dare, inda aƙalla ƴan bidiga hamsin ɗauke da muggan makamai, suka aikata ta’asarsu.
Ya ce, sun gudanar da kashe-kashen ne, ta hanyar shiga daga gida zuwa gida, suka rinƙa harbe mutane, inda ya ƙara da cewa, akwai gidan da ƴan bindigar, suka kashe ɗaukacin alhalin gidan, a cikin ɗakinsu na kwana.
Wasu da suka arce zuwa dazuka, domin tseratar da rayuwarsu, ƴan bindigar sun bi sahunsu, suka kuma hallaka su.
Ya ci gaba da cewa, duk a cikin daren ranar, akwai gidan da aka hallaka yara biyar, inda yaro ɗaya da ya rayu, ke kwance a Asibiti ake ci gaba da ceto rayuwarsa.
Bayan kwana ɗaya da aukuwar hare-haren, kafar yaɗa labarai ta waje ta AP, ta tuntuɓi kwamishinan trsaron cikin gida na Kaduna, kan kai hare-haren, sai dai, ya ka da baki ya ce, har yanzu, ba a yi masa cikaken bayani, kan lamarin ba.
Ƴan bindigar dai, sun gama cin Karesu babu babbaka sun kuma yi gaba, yayin da kuma ake ci gaba da ƙidayar yawan gawarwakin da aka hallaka
Harin na ƙauyen Naridon, ba shi ne, karo na farko ba, domin ƙungiyar CAN ta tabbatar da cewa, an kai irin waɗannan hare-haren ma, a wata Agustan 2025, inda aka hallaka mutane bakwai.
Haka zalika, a watan Yunin 2026, duk a ƙauyen na Naridon, wasu maharani sun kashe mutane tara tare da raunata mutane sha ɗaya.
Wannan, abin baƙin ciki ne, duba da cewa, a tsakanin watanni sha ɗaya a ƙauyen na Naridon, an gudanar da bizne mutane n agama gari, a cikin watanni sha ɗaya har karo na uku.
Bayan hari na ɗaya, na biyu har zuwa na uku a ƙauyen, babu wani abu, da ya sauya na ɗaukar ƙwararan matakai, daga ɓangaren mahukunta.
Sai dai, za a iya cewa, bayan harin na uku, gwamnan Kaduna ta umarci jami’an taro, da su ci gaba da ƙara ƙaimi na tabbatar da tsaro, inda kuma shugaban ƙasa, ya danganta kashe-kashen, a matsayin aikin ta’addanci.
Kazalika, ba wai hare-haren na ƙauyen Naridon kaɗai bane, akwai kuma wanda aka ƙaddamar da dare a ƙauyen Lajinge a Sokoto, a ranar 19 ga watan Yulin 2026, inda maharani, suka kashe mutane sha ɗaya, suka kuma ƙone wasu shida da ransu, a cikin gidajensu, ta hanyar yin amfani da Man Fetur.
Haka zalika, duk a cikin wannan makon, a wani hari da maharani suka kai a yankin Otukpo, na jihar Biniwe, sun hallaka mutane shida.
A cikin wasu jihohin ƙasar, a ƙasa da mako biyu, a wasu karkara na ƙasar, an bizne aƙalla mutane 58, kuma ba tare da wallafa cewar, an kama mutun ɗaya, da suka aikata kisan ba.
A kwanan baya dai, a Kaduna ƙungiyar gwanonin Arewacin ƙasar, ta ƙaddamar da wata gidauniya ta tsaro, bisa yin alƙawarin a duk wata kowacce jiha, za ta bayar da gudunmawar Naira biliyan ɗaya, a matsayin na ta gudunmawar.
Ta ƙaddamar da gidauniyar ce, mao biyu, kafin kai hare-haren na ƙauyen Naridon.
Haka zalika, ƙungiyar kare haƙƙin bil Adama ta ƙasa da ƙasa wato Amnesty International, da ke ci gaba da bibiyar irin waɗannan kashe-kashen, ta fitar da wani rahoton da ke nuna cewa, a jihohi bakwai na Arewacin ƙasar, a watan Mayun 2025, aƙalla an hallaka mutane 10,217 a cikin shekaru biyu kacal, a ƙarƙashin mulkin gwamnatin tarayya mai ci.
Rahoton ƙungiyar ya ce, jihar Biniwe, an hallaka kimanin mutane 6,900.
Sai dai, gwamnatin, ko kusa, ba ta son sanin waɗannan alƙaluman kuma ba ta ɗauki wasu ƙwararan matakai, na magance kai hare-haren ba.
A baya mun yi kira da a tura jami’an tsaro zuwa yankunan da ake yawan samun kai hare-haren, mun kuma yi kira da a samar da tsarin kai ɗaukin gaggawa na dakile hare-hare.
Kazalika, mun yi kira da samar da tsarin samun bayanan sirri, tare da tarwatsa sansanonin ƴan bindiga, mun yi kira da a hukunta duk wanda ke da hannu akai hare-haren.
A nan, za mu kuma sake yin waɗannan kiraye-kirayen, ba wai domin kiraye-kirayen sun yi ƙaranci ba, amma saboda yin gum ɗin na ƙin yin kiran, tamkar wata gazawa ce.
Alumomin da ke a karkara a yankunan Arewa maso Yamma, Arewa, ta tsakiya da kuma yankin tsakiyar Nijeriya wato Middle, na da haƙƙin kan gawamnati, na ta cika alawarin da ta yi masu, kafin wata waƙi’ar, ta ƙara aukuwa.
Idan har gwamnati za ta iya yin amfani da ɗimbin kuɗaɗe domin gudanar da wasu ayyukan da suka shafi ciyar da ƙasar gaba, shi menene ke hana ta, tabbatar da tsaro a mai ɗorewa, a ƙauyukan da ake yawan samun kai hare-haren ƴan bindiga?
Ya zama wajbi tun daga matakin fadar shugaban ƙasa da gwamnatin Kaduna, da sauran gwamnonin da ke a Arewa, su tashi haiƙan, domin tabbatar da tsaro, kafin a sake samun kai wasu hare-haren.
Kashe rayukan alummar da ba su ji ba su kuma gani ba a ƙauyen na Naridon, lamari ne, da wuce batun yin sharhi a Jirida kawai, amma sai idan har gwamnati ta nuna gaske take domin magance kai hare-haren.
Wannan Jaridar koda Tawadar Alƙamin zai ƙare, za ta ci gaba da yin rubuce-rubuce kan matsalar.














