Shugaban haɗaka na jam’iyyun adawa, Salihu Lukman, ya ce nasarar Ademola Adeleke a zaɓen gwamnan Jihar Osun da aka kammala kwanan nan ta nuna yadda jam’iyyun adawa za su iya kayar da Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu a zaɓen 2027.
Ya bayyana haka a cikin wata sanarwa a ƙarshen mako.
Rahotanin sun ruwaito cewa hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa, (INEC) ta bayyana Adeleke a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan Jihar Osun.
Ya doke ɗan takarar gwamnan jam’iyyar APC, Bola Oyebamiji.
Nasarar Adeleke ta ci gaba da yin martani daga ƴan Nijeriya da masu sharhi kan siyasa a cikin sa’o’i 24 da suka wuce.
A martanin, Lukman ya ce zaɓen Osun ya bayar da sahihan misali ga jam’iyyun adawa da ke neman kwashe kujerar Shugaba Tinubu a 2027.
Ya ƙara da cewa haɗin gwiwar jam’iyyun adawa ba ta rasa goyon bayan ƴan Nijeriya ba amma tana fuskantar ƙalubalen rabuwar kai.
A cewarsa, dole ne shugabannin ƴan adawa a Nijeriya su haɗu kai don kawar da Shugaba Tinubu.
“Jam’iyyun adawa a Nijeriya ba sa fama da ƙarancin goyon bayan jama’a. Babban ƙalubale gare su shi ne rarrabuwar kawuna daga shugabanninsu.
“Nijeriya tafi kowanne ɗan takara girma da kowanne buri da kowanne jam’iyya ta siyasa. Idan shugabannin adawa sun gaskata cewa ƙasar na buƙatar wani sabon shugabanci a 2027, to dole su nuna irin wannan jarumta da kiyaye kima da shirye-shiryen yarda wanda ya haifar da wannan sakamako a Osun,” in ji shi.














