ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Borrusia Dortmund Na Shirin Dawo Da Sancho Bayan Rashin Katabus A Man U

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
sancho

Borussia Dortmund na sha’awar sayen dan wasan gefe na Man U Jadon Sancho, inda ake tattaunawa kan yarjejeniyar aro har zuwa karshen kakar wasa ta bana.

United ta sayi Sancho daga Dortmund a shekara ta 2021 a kan kudi fam miliyan 73, amma kuma tun watan Agusta bai buga wa United wasa ko daya ba sakamakon rashin jituwar dake tsakaninsa da kocin kungiyar Eric Ten Hag.

Idan hakan ta tabbata Sancho zai koma kungiyar ta Borrusia Dortmund dake buga gasar Bundesliga a matsayin aro har zuwa karshen kakar wasanni ta bana.

ADVERTISEMENT
  • Man U Ta Maye Gurbin Eriksen Da Zai Yi Jinyar Watanni Uku
  • Bai Kamata Chelsea Ta Zauna A Matsayi Na 10 A Gasar Firimiya Ba – Pochettino

Man Utd ta sayi Sancho daga Dortmund a bazarar 2021 a kan fam miliyan 73 inda tun bayan zuwansa ya buga masu wasanni 58 inda ya jefa kwallaye 9 a raga.

Kwantiragin dan wasan na Ingila a Old Trafford zai kare ne a shekarar 2026, inda United ke da zabin tsawaitawa tsawon shekara guda.

LABARAI MASU NASABA

Makarantu Za Su Ci Gaba Da Zama A Rufe Har Sai Yanayin Tsaro Ya Inganta – Gwamnatin Kebbi

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

Tun lokacin da dan wasan mai shekaru 23 ya shiga shafukan sada zumunta inda ya karyata ikirarin da kocin kungiyar Eric Ten Hag ya yi na cewa Sancho yana atisaye shi kadai ba tare da sauran abokan wasansa ba ya sa ba a sake kiransa a cikin tawagar yan wasan kungiyar ba.

Abin lura a yanzu shi ne shin Borussia Dortmund za ta iya biyan cikakken albashin Jadon Sancho ko za su yi fatan United ta iya taimaka musu ta biya wani kaso na albashin dan wasan.

Idan zai tafi Dortmund na tsawon watanni shida, ya taka rawar gani kuma ya dawo Manchester United to tabbas darajar kasuwarsa za ta yi yawa fiye da yadda take a yanzu.

Sai dai a halin yanzu, akwai sauran aiki da yawa a kan wannan yarjejeniya, amma Borussia Dortmund tana sha’awar kuma tana tattaunawa da Manchester United kan Jadon Sancho.

sancho
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

MASU ALAKA

kebbi
Labarai

Makarantu Za Su Ci Gaba Da Zama A Rufe Har Sai Yanayin Tsaro Ya Inganta – Gwamnatin Kebbi

July 9, 2026
Ta’addanci
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

July 9, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Kyfatin Na Ƙasar Ghana ANDRE AYEW Na Fatan Kafa Tarihi A Gasar AFCON Ta Bana

Kyfatin Na Ƙasar Ghana ANDRE AYEW Na Fatan Kafa Tarihi A Gasar AFCON Ta Bana

LABARAI MASU NASABA

kebbi

Makarantu Za Su Ci Gaba Da Zama A Rufe Har Sai Yanayin Tsaro Ya Inganta – Gwamnatin Kebbi

July 9, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Shugabar Namibia

Li Qiang Ya Gana Da Shugabar Namibia

July 9, 2026
Xi Ya Bayar Da Umarni Dangane Da Gobarar Da Ta Tashi A Wani Kamfanin Sarrafa Takalma Dake Gabashin Kasar

Xi Ya Bayar Da Umarni Dangane Da Gobarar Da Ta Tashi A Wani Kamfanin Sarrafa Takalma Dake Gabashin Kasar

July 9, 2026
Ta’addanci

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

July 9, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Auto Draft

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

July 9, 2026
Auto Draft

DSS Ta Kama ‘Yar Jarida Zainab Sodiq Kan Zargin Mallakar Drone Ba Tare da Cikakkun Takardu ba

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

July 9, 2026
Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

July 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.