ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Sanya Ƴanmata A Kan Sana’a Kafin Aurar Da Su 

by Rabi'at Sidi Bala
8 months ago

Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Barkanmu da kasancewa tare da wannan fili mai albarka, wanda yake zaƙulo mana batutuwan da suke ci mana tuwo a kwarya. A yau zan yi magana a kan iyaye mata da maza, Ilimi da kuma sana’a. 

A wannan halin da muka tsinci kai ciki cikin wannan lokaci, ilimin ƴaƴa mata yana taimakawa sosai, haka ma sana’arsu. Ya kamata iyaye kafin su aurar da ƴa su tabbatar da sun nema mata waɗannan abubuwa guda biyu, lallai ta yi ilimin addini da na boko. A samu ma na bokon ya fi yawa, kuma kada a ruɗe ku a ce wai ƴar ku kar ta yi ilimin zamani, duk wannan an wuce wannan ‘Jahiliya period’.

ADVERTISEMENT
  • Kuskure Ne Daukar Harkar Fim A Matsayin Sana’a Kadai —Maryam CTV (2)
  • Gwamnan Kano Ya Yi Allah-wadai Da Kisan Uwa Da ‘Ya’yanta 6, Ya Umarci A Kamo Masu Laifin

In dai kana da iko da ƙarfi, ƴarka ta yi ilimi sosai, zai taimaketa har zaman aurenta, sannan sana’ar hannu ko ya take a tsaya a koye ta, wannan halin da muke ciki, da ilimin da sana’a zai taimakawa mijinta, ƴaƴanta da ku kanku iyayen. 

Saboda wasu a kan tunzurasu cewar da yarinya ta yi sakandari kawai a aurar da ita, wannan karatun me zai amfanar da ita, ba daidai ba ne ba. Likitoci gasu nan, wajen karɓar haihuwa, idan aka ce ƴaƴa mata ba za su yi karutu ba, to maza ne za su riƙa karɓar haihuwa.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Akwai ɓangarori da yawa, idan gida ne yarinyar ta kusa haihuwa, dole ana buƙatar taimakon matan, ba mazan ne za su yi ba. Sannan Ilimi yana da amfani ko da na addini ne, yana da amfani sosai, musamman ɓangaren wankan gawa da sauran abubuwa, yana da kyau a ce ƴaƴa mata suna shiga ɓangaren kada ace komai an barwa maza.

Dole ne mata su mayar da hankali sosai, yana rage lalacewar ƴaƴan zamani, sai an dogara da saurayi ya siya maka waya, ko ya siya miki lesin anko. Idan ki ka yi iliminki ko ki ka yi sana’arki, duk ya ishe ki, wallahi su kansu ƴan’iskan suna tsoron mace mai ilimi, suna tsoron mace mai sana’a, kuma ba za a faɗa mata abu ya ruɗe ta ba.

Dan haka yana da kyau lallai-lallai ilallah idan mata gareka ka nema  mata sana’ar da za ta yi, ta dogara da kanta, idan da dama ɗinma makarantar ma ta koma ta ɗan yi, domin za ta taimake ka, za ta taimaki ma ƴaƴanka. Iyaye ma a mayar da wannan hankalin, su kansu samari, ko kafin ka aureta ne, yi ƙoƙari ta yi karatun indai da hali zai taimake ku, ko na bokon ko na addinin.

Rabi'at Sidi Bala
+ postsBio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Yadda Alaƙata Da Adamu Zango Ta Bunƙasa A Kannywood —Jarumi Ibrahim Sodangi 
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Tsibirin Hainan Na Sin Ya Samu Bunkasar Cinikayya Karkashin Tsarin Jingine Harajin Sayayya

Tsibirin Hainan Na Sin Ya Samu Bunkasar Cinikayya Karkashin Tsarin Jingine Harajin Sayayya

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.