ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

by Sulaiman and Abba Ibrahim Wada
4 weeks ago
Arsenal

Abin mamaki ne yadda Arsenal ta fada cikin mawuyacin hali a baya-bayan nan, amma sai ga shi a yanzu ta kai wasan karshe na gasar Zakarun Turai ta Champions Leagu.

Matsi ya tattaru a kan Mikel Arteta domin ganin ya kawo karshen shekara 22 da kungiyar ta yi tana kamfar kofi.

Kokarin da suka nuna na kauce wa rashin yin nasara a dukkanin wasan da suka buga na Chamiopns League abu ne da har yanzu bai samu yabon da ya cancanta ba.

ADVERTISEMENT

Kwallon da Bukayo Saka ya jefa a raga kafin zuwa hutun rabin lokaci shi ne ya bai wa Arsenal nasarar da ta samu 1-0 a kan Atletico Madrid a daren ranar Talata, wanda hakan ke nufin an tashi da jimillar kwallaye Arsenal 2-1 Atletico Madrid daga wasa biyu da kungiyoyin suka buga.

A gaskiyar lamari, duk da cewa wasan da suka buga a filin wasa na Emirate bai kayatar sosai ba, Arsenal din ta yi kokari sosai a wasanninta na gasar Turai.

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

Arsenal ce kungiyar da har yanzu ba ta yi rashin nasara ba a gasar tun daga farkon wannan kaka, inda ta lallasa kungiyoyi kamar Bayern Munich da Inter Milan da kuma Sporting kafin kawowa wannan matsayi.

Kuma za a iya cewa Arsenal ta nuna rashin tausayi a wasanninta na gasar, kusan za a iya cewa babu wani lokaci da ta shiga wani babban hadarin da za a ce tana fargabar za a fitar da ita.

“Ba na tunanin wani zai raina kokarin da muka yi a wannan gasa har zuwa wannan lokaci,” in ji dan wasan tsakiya na kungiyar Declan Rice lokacin tattaunawarsa da Amazom Prime.

“Muna da hujjar da za mu yi murna a wannan lokaci. Gasa mafi daraja a kwallon kafa.”

“Gabanin fara wasan mun san irin hadarin da muke fuskanta, idan ba mu tunkare shi ba, to ba za ka iya tunkarar kowane wasan kwallon kafa ba.

Lokacin da muka ci kwallo ta farko, na san cewa za mu yi nasara. Na ji a jikina cewa wani muhimmin abu ya tunkaro mu.”

Magoya bayan Arsenal sun tarbi motar bas din da ta dauko ‘yan wasan da wasan tartsatsin wuta da sowa, wani abu da ba a saba gani ba – wani abu da mai horarwa Mikel Arteta ya bayyana a matsayin dare na musamman.

“Mun kafa tarihi gaba dayanmu,” in ji Arteta. “Na yi matukar farin ciki kuma ina alfahari da duk wanda ya taimaka wa wannan kungiya. Yadda aka tarbe mu a lokacin da muka iso abu ne na mausamman.

“Goyon bayan da aka nuna mana ya kara mana kuzari, ban taba ganin irin wannan lamari ba.”

“Mun san yadda kowa ke ji game da haka, ‘yan wasan sun yi duk abin da ya dace, kuma ga shi bayan shekara 20 a karo na biyu mun je wasan karashe na gasar Zakarun Turai ta Champions League.

Kokarin Arsenal a faifai

A ‘yan makonnin nan, Arsenal na ta kokarin samun nasarori a karshen kakar wasanni ta bana.

Bayan nasarar doke Fulham da ci uku da nema a karshen makon jiya, Arsenal ta da magoya bayanta sun bayyana farin ciki.

Wannan nasarar ta zo a daidai lokacin da ake nemanta, wato kafin wasan kungiyar na kusa da karshe. Sai kuma nasarar da ta samu ta zuwa wasan karshe na gasar Zakarun Turai. Wani karin arashin shi ne kwallo shida kawai aka zura a ragar kungiyar.

Da aka tambaye shi ko yana alfahari da nasarar da kungiyar ke samu, Arteta ya ce, “kwarai da gaske domin mun san karfin kungiyoyin da muka fafata da su a kowane mataki.”

“Atletico babbar kungiya ce kuma tana da karfi sosai. Mun san irin kokarin da take yi da irin rawar ganin da take nuna.”

 Ga yadda Arsenal ta kai wasan karshe:

Wasa 14 ta buga kuma ba a doke ta a ko daya ba a Zakarun na Turai. Wannan lokaci mafi tsawo da kungiyar ta yi ba tare da rashin nasara ba bayan wasa 13 da ta yi ba tare da rashin nasara ba a tsakanin watan Maris na 2005 zuwa Afrilun 2006.

Arsenal ta kai wasan karshe na Zakarun Turai a karon farko tun shekarar 2006. Wannan lokaci mafi tsawo da kungiya za ta kai wasan karshe a gasannin Turai manya biyu – Europa da Zakarun Turai – bayan Atletico da ta kai shekara 40 kafin ta kai wasan karshe a 2014.

A wasa 14 da Arsenal ta buga, ba a zura mata kwallo ba a guda tara.

Yiwuwar lashe kofuna biyu

Canjaras da Man City ta yi da Eberton ya kara ba Arsenal damar sa rai wajen lashe kofin Premier din ta bana.

City ta barar da babbar damar ce mako biyu bayan Arsenal ta yi rashin nasara a gasar, inda aka fara tunanin tamkar ta watsar da damar lashe gasar premier ta bana bayan dogon dako da ta yi.

Amma bayan doke Atlatico da kuma zama derere a saman teburin premier din da maki biyar, yanzu kusan za a iya cewa ta fi kusa da nasara.

“Irin kokarin da kungiyar nan take ta yi a cikin shekarun nan abin lura ne,” in ji Rice a lokacin da yake bayyana irin rawar da kungiyar ta taka a kaka uku da suka gaba da take karewa a ta biyu.

“Muna ta hakuri, muna ta aiki tukuru tare da goyon bayan kocinmu.”

Arteta ya ba mutane mamaki ganin yadda ya fara wasan da Myles Lewis-Skelly mai shekara 19 a tsakiya.

Haka kuma dan wasan gaba Biktor Gyokeres, wanda ya zura kwallo biyu a karshen makon jiya, ya nuna bajinta matuka, domin wasan na cikin wasannin da ya fi kwazo.

Rice na cikin ‘yanwasan da suka taimakon Arsenal a kakar bana, inda ko a wasan Atletico shi ne ya zama gwarzon danwasa.

Yanzu kallo ya fara komawa filin wasa na Emirate, inda ake sa ran watakila Arteta ya samu nasarar share wa magoya bayan Arsenal hawaye na samun kofi babba a kakar bana.

Arsenal
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Arsenal
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada

2027: Bukatar Zaben Shugabanni Na Gari

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.