Rahotanni daga PUNCH Sports Edtra sun ce Nijeriya ta lashe jimillar lambobin yabo 16 a gasar cin kofin Afirka na Tseren Keke ta Confederation of African Cycling Para-Track and Track African Championships na wannan shekarar da aka gudanar a birnin Abuja, gasar wacce aka gudanar a filin wasa na Moshood Abiola National Stadium ta tattaro fitattun masu tseren kekuna daga ko’ina cikin nahiyar, ciki har da Masar, Kenya, Afirka ta Kudu, Aljeriya da kuma mai masaukin baki Nijeriya.
Bayan kwanaki biyu ana gasar, Nijeriya ce ke kan gaba a teburin lambobin yabo, inda ta samu kyautar zinare 9, azurfa 5 da tagulla 2, wanda hakan ya sanya ta zama a sahun gaba, Masar ce ke matsayi na biyu da lambobin yabo 14, yayin da Kenya ke matsayi na uku da lambar yabo 9, rawar da tawagar Nijeriya ta taka ya samu karbuwa daga magoya baya a filin wasan, inda yan gasar sukayi fice wajen juriya da fasaha a duk lokacin da ake gasar.
Gasar ta kuma janyo yabo daga masu bibiyar wasan inda sukace yanayin ingancin kayayyakin aiki da akayi amfani dasu a Abuja ya burgesu, kafin yanzu Nijeriya ta karbi bakuncin gasar a tsakanin shekarar 2021 da 2023, wanda hakan ya kara karfafa matsayinta na zama babbar cibiyar da za a yi amfani da ita wajen gudanar da gasar keke ta Afirka, gasar wannan shekarar ya jawo hankalin masu kekuna sama da 100 daga kasashe takwas, dukkansu suna fafatawa domin samun lambar yabo ta nahiyar.















Discussion about this post