Shugaba Bola Ahmed Tinubu na Nijeriya ya amince da bukatar karbar bakuncin Babban Taron Hukumar kwallon kafa ta nahiyar Afirika mai dauke da kasashe 54 wanda kuma ya hada da bikin bayar da kyaututtuka na CAF na shekarar 2026, an tabbatar da amincewar ne a cikin wata sanarwa da Daraktan Sadarwa na Hukumar Kwallon Kafa ta Nijeriya, Ademola Olajire ya fitar, a cewar sanarwar Shugaban ya sanar da amincewar ne a lokacin taron kasashen Afrika da aka gudanar a birnin Nairobi na kasar Kenya, bayan haduwa da Shugaban CAF Patrice Motsepe.
Wadanda suka halarci taron sun hada da Ministar Harkokin Waje ta Nijeriya, Bianca Odumegwu-Ojukwu, Shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Nijeriya, Ibrahim Musa Gusau, Babban mai bayar da shawara na Musamman ga Shugaban CAF, Amaju Melbin Pinnick, da kuma Mukaddashin Sakatare Janar na CAF, Samson Adamu.
Babban taron CAF karo na 48, wanda aka shirya gudanarwa a watan Oktoba, zai tattaro manyan masu ruwa da tsaki a harkar kwallon kafa ta Afirka, ciki har da shugabannin kungiyoyin CAF guda 54, wakilan shiyyoyi 6 na CAF da kuma sauran masu gudanar da kwallon kafa, da manyan jami’ai daga fadin nahiyar.
Ana daukar taron a matsayin daya daga cikin muhimman taruka a kwallon kafa ta Afirka, inda ake tattaunawa da amincewa da manyan shawarwari game da ci gaba da gudanar da wasan kwallon kafa a nahiyar Afirika, nasarar da Nijeriya ta samu na karbar bakuncin taron ya kara nuna tasirin da kasar ke da shi a cikin harkokin kwallon kafa ta Afirka.
Baya ga taron, Nijeriya za ta kuma karbi bakuncin bikin bayar da kyaututtuka na CAF, daya daga cikin manyan taruka da hukumar ta CAF ke Shiryawa a kowace shekara inda ake zabo zakakurai a fannoni da dama na kwallon kafa domin karramasu, bikin na shekara-shekara yana zakulo fitattun yan wasa a kwallon kafa ta Afirka, ciki har da yan wasa, masu horarwa, kungiyoyin kwallon kafa da masu gudanar da kwallon kafa wanda manyan yan wasan kwallon kafa na Duniya da manyan mutane suka halarta.
Masu ruwa da tsaki a harkar wasanni a Nijeriya sun bayyana nasarar a matsayin babban ci gaba da Nijeriya ta samu wanda zai sake janyo masu zuba jari a harkar kwallon kafa tare da tsammanin cewa abubuwan da za su faru za su jawo hankalin kasashen Duniya da kuma karfafa ayyukan tattalin arziki a cikin birnin Abuja Wanda shine mai masaukin baki, amincewar ta kuma nuna dangantakar dake tsakanin hukumomin kwallon kafa na Nijeriya da shugabancin CAF a karkashin Motsepe.















Discussion about this post