ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana

by Abba Ibrahim Wada
2 months ago
CAF

Shugaba Bola Ahmed Tinubu na Nijeriya ya amince da bukatar karbar bakuncin Babban Taron Hukumar kwallon kafa ta nahiyar Afirika mai dauke da kasashe 54 wanda kuma ya hada da bikin bayar da kyaututtuka na CAF na shekarar 2026, an tabbatar da amincewar ne a cikin wata sanarwa da Daraktan Sadarwa na Hukumar Kwallon Kafa ta Nijeriya, Ademola Olajire ya fitar, a cewar sanarwar Shugaban ya sanar da amincewar ne a lokacin taron kasashen Afrika da aka gudanar a birnin Nairobi na kasar Kenya, bayan haduwa da Shugaban CAF Patrice Motsepe.

Wadanda suka halarci taron sun hada da Ministar Harkokin Waje ta Nijeriya, Bianca Odumegwu-Ojukwu, Shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Nijeriya, Ibrahim Musa Gusau, Babban mai bayar da shawara na Musamman ga Shugaban CAF, Amaju Melbin Pinnick, da kuma Mukaddashin Sakatare Janar na CAF, Samson Adamu.

Babban taron CAF karo na 48, wanda aka shirya gudanarwa a watan Oktoba, zai tattaro manyan masu ruwa da tsaki a harkar kwallon kafa ta Afirka, ciki har da shugabannin kungiyoyin CAF guda 54, wakilan shiyyoyi 6 na CAF da kuma sauran masu gudanar da kwallon kafa, da manyan jami’ai daga fadin nahiyar.

ADVERTISEMENT

Ana daukar taron a matsayin daya daga cikin muhimman taruka a kwallon kafa ta Afirka, inda ake tattaunawa da amincewa da manyan shawarwari game da ci gaba da gudanar da wasan kwallon kafa a nahiyar Afirika, nasarar da Nijeriya ta samu na karbar bakuncin taron ya kara nuna tasirin da kasar ke da shi a cikin harkokin kwallon kafa ta Afirka.

Baya ga taron, Nijeriya za ta kuma karbi bakuncin bikin bayar da kyaututtuka na CAF, daya daga cikin manyan taruka da hukumar ta CAF ke Shiryawa a kowace shekara inda ake zabo zakakurai a fannoni da dama na kwallon kafa domin karramasu, bikin na shekara-shekara yana zakulo fitattun yan wasa a kwallon kafa ta Afirka, ciki har da yan wasa, masu horarwa, kungiyoyin kwallon kafa da masu gudanar da kwallon kafa wanda manyan yan wasan kwallon kafa na Duniya da manyan mutane suka halarta.

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Masu ruwa da tsaki a harkar wasanni a Nijeriya sun bayyana nasarar a matsayin babban ci gaba da Nijeriya ta samu wanda zai sake janyo masu zuba jari a harkar kwallon kafa tare da tsammanin cewa abubuwan da za su faru za su jawo hankalin kasashen Duniya da kuma karfafa ayyukan tattalin arziki a cikin birnin Abuja Wanda shine mai masaukin baki, amincewar ta kuma nuna dangantakar dake tsakanin hukumomin kwallon kafa na Nijeriya da shugabancin CAF a karkashin Motsepe.

CAF
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
A Karon Farko Mahajjatan Zamfara Sun Tashi Daga Jiharsu

A Karon Farko Mahajjatan Zamfara Sun Tashi Daga Jiharsu

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.