ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana

by Abba Ibrahim Wada
1 month ago
CAF

Shugaba Bola Ahmed Tinubu na Nijeriya ya amince da bukatar karbar bakuncin Babban Taron Hukumar kwallon kafa ta nahiyar Afirika mai dauke da kasashe 54 wanda kuma ya hada da bikin bayar da kyaututtuka na CAF na shekarar 2026, an tabbatar da amincewar ne a cikin wata sanarwa da Daraktan Sadarwa na Hukumar Kwallon Kafa ta Nijeriya, Ademola Olajire ya fitar, a cewar sanarwar Shugaban ya sanar da amincewar ne a lokacin taron kasashen Afrika da aka gudanar a birnin Nairobi na kasar Kenya, bayan haduwa da Shugaban CAF Patrice Motsepe.

Wadanda suka halarci taron sun hada da Ministar Harkokin Waje ta Nijeriya, Bianca Odumegwu-Ojukwu, Shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Nijeriya, Ibrahim Musa Gusau, Babban mai bayar da shawara na Musamman ga Shugaban CAF, Amaju Melbin Pinnick, da kuma Mukaddashin Sakatare Janar na CAF, Samson Adamu.

Babban taron CAF karo na 48, wanda aka shirya gudanarwa a watan Oktoba, zai tattaro manyan masu ruwa da tsaki a harkar kwallon kafa ta Afirka, ciki har da shugabannin kungiyoyin CAF guda 54, wakilan shiyyoyi 6 na CAF da kuma sauran masu gudanar da kwallon kafa, da manyan jami’ai daga fadin nahiyar.

ADVERTISEMENT

Ana daukar taron a matsayin daya daga cikin muhimman taruka a kwallon kafa ta Afirka, inda ake tattaunawa da amincewa da manyan shawarwari game da ci gaba da gudanar da wasan kwallon kafa a nahiyar Afirika, nasarar da Nijeriya ta samu na karbar bakuncin taron ya kara nuna tasirin da kasar ke da shi a cikin harkokin kwallon kafa ta Afirka.

Baya ga taron, Nijeriya za ta kuma karbi bakuncin bikin bayar da kyaututtuka na CAF, daya daga cikin manyan taruka da hukumar ta CAF ke Shiryawa a kowace shekara inda ake zabo zakakurai a fannoni da dama na kwallon kafa domin karramasu, bikin na shekara-shekara yana zakulo fitattun yan wasa a kwallon kafa ta Afirka, ciki har da yan wasa, masu horarwa, kungiyoyin kwallon kafa da masu gudanar da kwallon kafa wanda manyan yan wasan kwallon kafa na Duniya da manyan mutane suka halarta.

LABARAI MASU NASABA

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

Masu ruwa da tsaki a harkar wasanni a Nijeriya sun bayyana nasarar a matsayin babban ci gaba da Nijeriya ta samu wanda zai sake janyo masu zuba jari a harkar kwallon kafa tare da tsammanin cewa abubuwan da za su faru za su jawo hankalin kasashen Duniya da kuma karfafa ayyukan tattalin arziki a cikin birnin Abuja Wanda shine mai masaukin baki, amincewar ta kuma nuna dangantakar dake tsakanin hukumomin kwallon kafa na Nijeriya da shugabancin CAF a karkashin Motsepe.

CAF
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
Wasanni

FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

June 21, 2026
Next Post
A Karon Farko Mahajjatan Zamfara Sun Tashi Daga Jiharsu

A Karon Farko Mahajjatan Zamfara Sun Tashi Daga Jiharsu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.