ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana

by Abba Ibrahim Wada
3 weeks ago
CAF

Shugaba Bola Ahmed Tinubu na Nijeriya ya amince da bukatar karbar bakuncin Babban Taron Hukumar kwallon kafa ta nahiyar Afirika mai dauke da kasashe 54 wanda kuma ya hada da bikin bayar da kyaututtuka na CAF na shekarar 2026, an tabbatar da amincewar ne a cikin wata sanarwa da Daraktan Sadarwa na Hukumar Kwallon Kafa ta Nijeriya, Ademola Olajire ya fitar, a cewar sanarwar Shugaban ya sanar da amincewar ne a lokacin taron kasashen Afrika da aka gudanar a birnin Nairobi na kasar Kenya, bayan haduwa da Shugaban CAF Patrice Motsepe.

Wadanda suka halarci taron sun hada da Ministar Harkokin Waje ta Nijeriya, Bianca Odumegwu-Ojukwu, Shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Nijeriya, Ibrahim Musa Gusau, Babban mai bayar da shawara na Musamman ga Shugaban CAF, Amaju Melbin Pinnick, da kuma Mukaddashin Sakatare Janar na CAF, Samson Adamu.

Babban taron CAF karo na 48, wanda aka shirya gudanarwa a watan Oktoba, zai tattaro manyan masu ruwa da tsaki a harkar kwallon kafa ta Afirka, ciki har da shugabannin kungiyoyin CAF guda 54, wakilan shiyyoyi 6 na CAF da kuma sauran masu gudanar da kwallon kafa, da manyan jami’ai daga fadin nahiyar.

ADVERTISEMENT

Ana daukar taron a matsayin daya daga cikin muhimman taruka a kwallon kafa ta Afirka, inda ake tattaunawa da amincewa da manyan shawarwari game da ci gaba da gudanar da wasan kwallon kafa a nahiyar Afirika, nasarar da Nijeriya ta samu na karbar bakuncin taron ya kara nuna tasirin da kasar ke da shi a cikin harkokin kwallon kafa ta Afirka.

Baya ga taron, Nijeriya za ta kuma karbi bakuncin bikin bayar da kyaututtuka na CAF, daya daga cikin manyan taruka da hukumar ta CAF ke Shiryawa a kowace shekara inda ake zabo zakakurai a fannoni da dama na kwallon kafa domin karramasu, bikin na shekara-shekara yana zakulo fitattun yan wasa a kwallon kafa ta Afirka, ciki har da yan wasa, masu horarwa, kungiyoyin kwallon kafa da masu gudanar da kwallon kafa wanda manyan yan wasan kwallon kafa na Duniya da manyan mutane suka halarta.

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

Masu ruwa da tsaki a harkar wasanni a Nijeriya sun bayyana nasarar a matsayin babban ci gaba da Nijeriya ta samu wanda zai sake janyo masu zuba jari a harkar kwallon kafa tare da tsammanin cewa abubuwan da za su faru za su jawo hankalin kasashen Duniya da kuma karfafa ayyukan tattalin arziki a cikin birnin Abuja Wanda shine mai masaukin baki, amincewar ta kuma nuna dangantakar dake tsakanin hukumomin kwallon kafa na Nijeriya da shugabancin CAF a karkashin Motsepe.

CAF
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
A Karon Farko Mahajjatan Zamfara Sun Tashi Daga Jiharsu

A Karon Farko Mahajjatan Zamfara Sun Tashi Daga Jiharsu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.