• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Samar Da Cikkakken Tsaro Ga Hukumar Zabe

by Leadership Hausa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Bukatar Samar Da Cikkakken Tsaro Ga Hukumar Zabe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daga dukkan alamu akwai wani shiri na musamman daga wasu makiya tsarin dimukradiyya na ganin sun yi wa kokarin Hukumar Zabe INEC na gudanar da sahihin zabe  zagon kasa.

Hare-haren ban takaici da ake kai wa ofishoshin hukumar a sassan kasar a ‘yan wattanin nan alamu ne da ke nuni da yin hakan.

  • Yadda Gwamnonin Nijeriya Suka Butulce Wa Shugaba Buhari Bayan Ya Fitar Da Su Kunya
  • Sin Za Ta Ci Gaba Da Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Warware Rikici Cikin Lumana Ta Hanyarta

A makon da ya gabata ne, wasu da ba a kai ga gane ko su wanene ba su ka kai hari tare da kone ofishin INEC a Jihar Ogun bayan sun fi karfin masu gadin ofishin. Rahottanin sun nuna cewa, an lalata ginin ofishin da wasu kayyakin aiki da suka hada da akwatun zabe 904 gurbin kebewa don kada kuri’a guda 29, amsa kuwa 30 da jakankunan zabe 57 da kuma akwatun samar da 8, sauran sun hada da katin zabe na dindindin 65,699.

Haka kuma Kwamishinan zabe na JIhar Osun, Mutiu Agboke, ya sanar da cewa, an banka wa ofishin hukumar da ke karamar hukumar Ede ta Kudu wuta. Idan kuma za a iya tunawa ‘yan daba sun kona ofishin INEC da ke karamar hukumar Igbo-Eze a Jihar Inugu da ke yankin Kudu maso Gabashin Nijeriya.

Hukumar ta sanar da cewa, duk da cewa babu wani mutujm da ya rasa ransa amma an lalata akwatun zabe 748, wurin kebewa don kada kuri’a guda 240 kayyakin amfani na ofis duk da kokarin da ofishin kashe gobara na Jihar Inugu daga garin Nsukka suka yi don shawo kan gobarar.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

Bayani ya kuma nuna cewa a watan Afrilu na wannan shekarar, ta sanar da cewa, ta yi asarar na’urrar ‘card reader’ da ya fi guda 99,836 a hare-haren da aka kai mata har guda 42 a ofsihoshinta da wadanda aka kai wa ma’aikatan a cikin shekara uku. Hakanan haka a wasu bayanai da INEC ta bayar ta sanar da cewa, ya zuwa watan Mayu na shekarar 2021, an kai mata hare-hare da suka kai 41 a jihohi 14 a fadin tayayyar kasar nan a tsakanin shekarar 2019 zuwa 2021. A shekarar 2019 kawai, hukumar zaben ta fuskanci hare- hare 9 a jihohi 4, a shekarar 2020 kuma ta fuskanci hare hare 21 a jihohi 9 haka kuma a shekarar 2021 an bayar da rahoto 11 a jihohi 7 na tarayyar kasar nan. A rahoton INEC ta bayyana cewa, hare-haren ya kunshi kone-kone da lalata mata kayyaki.

Yadda kone-konen ke kara karuwa akan ofishoshin INEC da kuma mugun nufi wadanda ke kai hare-haren ya fara tayar da hankulan al’ummar kasa har ana tunanin za su iya shafar sahihancin babban zaben shekarar 2023. Ra’ayin wannan jaridar shi ne lallai wadannan hare haren a bayyane yake cewa da gangan ne ake yin su da nufin tsotara wasu al’umma daga kada kuri’a tun ma kafin a fara harkar zaben.

A nasu bangaren, kasashen Birtaniya da Amurka sun nuna damuwarsu ga hare-haren da ake kai wa ofishoshin INEC da yadda ake lalata kayyanin aiki su a fadin tarayyar kasar nan, sun kuma yi gargadin cewa, lallai wannan babbar barazana ce ga zabukkan 2023 kuma barazana ce ga ita kanta harkar dimokradiyya da kanta.

Duk da hukumar bata huta ba wajen ganin ta gudanar da sahihin zabe ta hanyar samar da hanyar aika da sakamakon zabe ta na’ura mai kwakwalwa da na’urar BIBAS amma wasu ‘yan siyasa sun dukufa wajen yin zargin kara ga wannan shiri na hukumar zaben ta hanyar kai hare-hare a kan kayan aikin hukumar INEC musamman a wuraren da suke ganin basu da magoya baya masu yawa, abokan hamayyar su ne ke da mafi yawn al’ummar da ke a yankin.

Wani karin abin damuwa a nan kuma shi ne mastalar tsaron da ake fuskanta a wasu sassan kasar nan. Muna daukar wadannan matsalolin guda biyu a matsayin abubuwan da za su iya shafar yadda za a gudanar da sahihin zabe cikin kwanciyar hankalin a 2023.

Tuni rahoto ya nuna cewa, akwai wasu al’umma fiye da 686 da suke karkashin ikon ‘yanbindga. Idan za a iya tunawa a watan Yuni na wananan shekarar ne, kungiyar ‘yan ta’adda ta Ansaru suka haramta harkokin siyasa a masarautar Birnin Gwari da ke Jihar Kaduna. Haka kuma matsalar a yankin Arewancin Nijeriya ya tarwatsa miliyoyin al’umma da gidajensu na gado. Shugaba Muhammadu Buhari ya umarci jami’an tsaro su tabbatar da samar da tsaro daga nan zuwa ranar 31 ga watan Disamba. Muna fatar Allah ya basu nasarar samar da cikakken zaman lafiya.

Tabbas mun ji dadin yadda aka samar da karin matakan tsaro a ofishishin INEC a sassan Nijeriya don kare aukuwar karin hare-haren ake yi.

Bayani ya nuna cewa, an samar da jami’an ‘yansanda, sojoji, DSS da jami’an hukumar kashe gobara don kare ofishoshin na INEC a sassan Nijeriya. Haka kuma Babban Sufeton ‘Yansanda, Usman Alkali, ya umarci Kwamishinonin ‘yansanda su samar da shirin tsaro na musamman don kare ofishoshin INEC a fadin tarayyar kasar nan.

A kan wadannan matsololin muke kira ga jami’an tsaro tabbatar da kamawa tare da hukunta dukkan wadanda aka samu da aikata laifin kai hari ofishoshin hukumar zabe ta INEC. Tabbas masu kai hare-haren nan ba aljannu ba ne. Yakamata a tona masu asiri a kuma hukunta su. Sun cigaba da kai hare-haren ne don babu wanda aka kama aka kuma hukunta. A ra’ayinmu in har aka kai ga kama ‘yansiyasar da ke daukar nauyin masu kai hare-haren tare da hukunta su, to zai taimaka wajen rage hare-haren da ake kaiwa.

A matsayinmu na gidan jarida, muna tsaye a kan bukatar gudanar da sahihin zabe, fatanmu shi ne tabbatar da ra’ayin al’umma ce ke yin galaba a zabukkan da za a gudanar. A ra’ayinmmu kuma daya daga cikin hanyoyin da za a iya cimma wannan burin shi ne tabbatar da cikakken tsaro ga ma’aikata da dukkan kayyakin zabe da INEC ta tanada.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECTsaroZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Gwamnonin Nijeriya Suka Butulce Wa Shugaba Buhari Bayan Ya Fitar Da Su Kunya

Next Post

Zaben Shugaban Kasa: Kallo Ya Koma Kan INEC

Related

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Manyan Labarai

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

28 minutes ago
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
Da ɗumi-ɗuminsa

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

10 hours ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Da ɗumi-ɗuminsa

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

11 hours ago
Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar

12 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Da ɗumi-ɗuminsa

Lauyoyin Majalisar Dattawa Sun Ƙaryata Natasha Kan Cewa Kotu Ta Ce Ta Koma Bakin Aiki

15 hours ago
Namadi Sambo Ya Yaba Wa Gwamna Abba Yusuf Kan Bunƙasa Ɓangaren Ilimi Da Gine-Gine A Kano
Manyan Labarai

Namadi Sambo Ya Yaba Wa Gwamna Abba Yusuf Kan Bunƙasa Ɓangaren Ilimi Da Gine-Gine A Kano

16 hours ago
Next Post
Zaben Shugaban Kasa: Kallo Ya Koma Kan INEC

Zaben Shugaban Kasa: Kallo Ya Koma Kan INEC

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.