ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

by Abubakar Abba
2 months ago

Cibiyar binciken harkar noma ta Jami’ar Ahamadu Bello da ke Zariya (IAR), na gudanar da ayyukan bincike sama da 140 kan ayyukan noma.

Kazalika, cibiyar ta kuma gabatar da sabbin ayyuka 19, kan kakar aikin noma ta 2026, inda ayyukan suka kai jimillar 159.

Farfesa Ado Yusuf, Daraktan Cibiyar, ya sanar da haka ne yayin taron bita, wanda ya haɗa da na shiyya, wato REFILS, domin yin nazari kan binciken aikin na 2026 da aka saba gudanarwa a duk shekara.

ADVERTISEMENT

Taron, wanda ya gudana a cibiyar da ke jami’ar Ahmadu Bello da ke Samaru a garin na Zariya, Farfesa Nafi’u Abdu Yusuf, Mataimakin Daraktan Cibiyar ne ya wakilci Farfesa Ado Yusuf.

Ya yi nuni da cewa, a ɗaukacin faɗin duniya, ana ci gaba fuskantar ƙalubalen sauyin yanayi, ƙarancin ruwan sama da kuma saurin ɗaukewar ruwan sama.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Ya ƙara da cewa, saboda waɗannan matsalolin, akwai buƙatar a gudanar da binciken, domin lalubo da mafita a kan ƙalubalen.

Ya ci gaba da cewa, ayyukan binciken da cibiyar ta gudanar a 2026, cibiyar ta mayar da hankali ne a kan nauyin da aka ɗora mata kan yin binciken amfanin gona da nufin gano nau’ikan amfanin na gona da za su iya jurewa kowane irin yanayi.

A cewarsa, aikin zai taimaka wajen ƙara samarwa da manoman ƙasar nan kuɗaɗen shiga da kuma ƙara haɓaka samar da wadatacccen abinci a ƙasar.

Ya ce, cibiyar shekaru sama da goma da suka gabata, na ci gaba da ksancewa ɗaya tilo a ƙasar, wacce ta ci gaba da fitar da nau’ika amfanin gona ga manoman ƙasar.

“A 2026 kacal, cibiyar ta fitar da nau’ikan amfanin gona na farin wake guda huɗu da suka haɗa da SAMPEA 22, SAMPEA 23, SAMPEA 24 da kuma SAMPEA 25,” In ji Daraktan.

Ya ƙara da cewa, cibiyar ta kuma fitar da wasu nau’ikan na masara guda biyu, SAMMAZ 78 da kuma na Gyaɗa, SAMNUT 30, tare da ƙarin wasu nau’ikan na Auduga guda huɗu da na masara guda tara, waɗanda aka fitar ta hanyar haɗaka tsakanin ƙungiyar aikin noma ta ƙasa da ƙasa da kuma kamfanonin cikin gida masu sarrafa Irin noma.

Ya kuma yi na’am, kan damar da Gwamnatin Jihar Ribas ta bayar, na amincewa da kafa cibiyar gudanar da binciken aikin noma, domin amfanin ƴan jihar.

Daraktan, ya kuma miƙa ƙoƙon bara ga ɗaukacin gwamnatocin da ke Arewacin ƙasar, da su yi koyi da gwamnatin ta Ribas.

A nasa jawabin, Farfesa Adamu Ahmed, Shugaban Jami’ar ABU, ya buƙaci mahalarta taron bitar da cewa, ba wai kaɗai mayar da hankalai kan samar da wadataccen abinci a ƙasar ba, su tabbata sun lalubo da wasu hanyoyin ingancin abininci, ta hanyar gudanar da bincike wanda hakan zai amfani ɗaukacin al’ummar ƙasar.

Adamu, wanda Mataimakinsa Farfesa Bello Sabo, ya wakilta a wajen taron, ya yi nuni da cewa, za a iya daƙile yunwa da ƙarancin abinci mai gina jiki ne kaɗai a ƙasar, ta hanyar zuba hannun jari a ɓangaren gudanar da bincike.

“Ina mai kira a gare ku, ba wai kaɗai gudanar da bincke ba, domin wallafawa ba, amma akwai matuƙar buƙatar lalubo da mafita kan ragewa ƴan ƙasar matsin tattalin arziƙin da suke ci gaba da fuskanta, ta hanyar yin amfani da fasahar kimiyyar zamani,” a cewar Adamu.

Taken taron bitar shi ne, rage ƙalubalen sauyin yanayin da ke haifar da illa a fannin aikin noma tare da ƙarfafa samar da wadataccen abinci.

Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.