Cibiyar binciken harkar noma ta Jami’ar Ahamadu Bello da ke Zariya (IAR), na gudanar da ayyukan bincike sama da 140 kan ayyukan noma.
Kazalika, cibiyar ta kuma gabatar da sabbin ayyuka 19, kan kakar aikin noma ta 2026, inda ayyukan suka kai jimillar 159.
Farfesa Ado Yusuf, Daraktan Cibiyar, ya sanar da haka ne yayin taron bita, wanda ya haɗa da na shiyya, wato REFILS, domin yin nazari kan binciken aikin na 2026 da aka saba gudanarwa a duk shekara.
Taron, wanda ya gudana a cibiyar da ke jami’ar Ahmadu Bello da ke Samaru a garin na Zariya, Farfesa Nafi’u Abdu Yusuf, Mataimakin Daraktan Cibiyar ne ya wakilci Farfesa Ado Yusuf.
Ya yi nuni da cewa, a ɗaukacin faɗin duniya, ana ci gaba fuskantar ƙalubalen sauyin yanayi, ƙarancin ruwan sama da kuma saurin ɗaukewar ruwan sama.
Ya ƙara da cewa, saboda waɗannan matsalolin, akwai buƙatar a gudanar da binciken, domin lalubo da mafita a kan ƙalubalen.
Ya ci gaba da cewa, ayyukan binciken da cibiyar ta gudanar a 2026, cibiyar ta mayar da hankali ne a kan nauyin da aka ɗora mata kan yin binciken amfanin gona da nufin gano nau’ikan amfanin na gona da za su iya jurewa kowane irin yanayi.
A cewarsa, aikin zai taimaka wajen ƙara samarwa da manoman ƙasar nan kuɗaɗen shiga da kuma ƙara haɓaka samar da wadatacccen abinci a ƙasar.
Ya ce, cibiyar shekaru sama da goma da suka gabata, na ci gaba da ksancewa ɗaya tilo a ƙasar, wacce ta ci gaba da fitar da nau’ika amfanin gona ga manoman ƙasar.
“A 2026 kacal, cibiyar ta fitar da nau’ikan amfanin gona na farin wake guda huɗu da suka haɗa da SAMPEA 22, SAMPEA 23, SAMPEA 24 da kuma SAMPEA 25,” In ji Daraktan.
Ya ƙara da cewa, cibiyar ta kuma fitar da wasu nau’ikan na masara guda biyu, SAMMAZ 78 da kuma na Gyaɗa, SAMNUT 30, tare da ƙarin wasu nau’ikan na Auduga guda huɗu da na masara guda tara, waɗanda aka fitar ta hanyar haɗaka tsakanin ƙungiyar aikin noma ta ƙasa da ƙasa da kuma kamfanonin cikin gida masu sarrafa Irin noma.
Ya kuma yi na’am, kan damar da Gwamnatin Jihar Ribas ta bayar, na amincewa da kafa cibiyar gudanar da binciken aikin noma, domin amfanin ƴan jihar.
Daraktan, ya kuma miƙa ƙoƙon bara ga ɗaukacin gwamnatocin da ke Arewacin ƙasar, da su yi koyi da gwamnatin ta Ribas.
A nasa jawabin, Farfesa Adamu Ahmed, Shugaban Jami’ar ABU, ya buƙaci mahalarta taron bitar da cewa, ba wai kaɗai mayar da hankalai kan samar da wadataccen abinci a ƙasar ba, su tabbata sun lalubo da wasu hanyoyin ingancin abininci, ta hanyar gudanar da bincike wanda hakan zai amfani ɗaukacin al’ummar ƙasar.
Adamu, wanda Mataimakinsa Farfesa Bello Sabo, ya wakilta a wajen taron, ya yi nuni da cewa, za a iya daƙile yunwa da ƙarancin abinci mai gina jiki ne kaɗai a ƙasar, ta hanyar zuba hannun jari a ɓangaren gudanar da bincike.
“Ina mai kira a gare ku, ba wai kaɗai gudanar da bincke ba, domin wallafawa ba, amma akwai matuƙar buƙatar lalubo da mafita kan ragewa ƴan ƙasar matsin tattalin arziƙin da suke ci gaba da fuskanta, ta hanyar yin amfani da fasahar kimiyyar zamani,” a cewar Adamu.
Taken taron bitar shi ne, rage ƙalubalen sauyin yanayin da ke haifar da illa a fannin aikin noma tare da ƙarfafa samar da wadataccen abinci.















Discussion about this post