ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

by Abubakar Abba
2 weeks ago

Cibiyar binciken harkar noma ta Jami’ar Ahamadu Bello da ke Zariya (IAR), na gudanar da ayyukan bincike sama da 140 kan ayyukan noma.

Kazalika, cibiyar ta kuma gabatar da sabbin ayyuka 19, kan kakar aikin noma ta 2026, inda ayyukan suka kai jimillar 159.

Farfesa Ado Yusuf, Daraktan Cibiyar, ya sanar da haka ne yayin taron bita, wanda ya haɗa da na shiyya, wato REFILS, domin yin nazari kan binciken aikin na 2026 da aka saba gudanarwa a duk shekara.

ADVERTISEMENT

Taron, wanda ya gudana a cibiyar da ke jami’ar Ahmadu Bello da ke Samaru a garin na Zariya, Farfesa Nafi’u Abdu Yusuf, Mataimakin Daraktan Cibiyar ne ya wakilci Farfesa Ado Yusuf.

Ya yi nuni da cewa, a ɗaukacin faɗin duniya, ana ci gaba fuskantar ƙalubalen sauyin yanayi, ƙarancin ruwan sama da kuma saurin ɗaukewar ruwan sama.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Ya ƙara da cewa, saboda waɗannan matsalolin, akwai buƙatar a gudanar da binciken, domin lalubo da mafita a kan ƙalubalen.

Ya ci gaba da cewa, ayyukan binciken da cibiyar ta gudanar a 2026, cibiyar ta mayar da hankali ne a kan nauyin da aka ɗora mata kan yin binciken amfanin gona da nufin gano nau’ikan amfanin na gona da za su iya jurewa kowane irin yanayi.

A cewarsa, aikin zai taimaka wajen ƙara samarwa da manoman ƙasar nan kuɗaɗen shiga da kuma ƙara haɓaka samar da wadatacccen abinci a ƙasar.

Ya ce, cibiyar shekaru sama da goma da suka gabata, na ci gaba da ksancewa ɗaya tilo a ƙasar, wacce ta ci gaba da fitar da nau’ika amfanin gona ga manoman ƙasar.

“A 2026 kacal, cibiyar ta fitar da nau’ikan amfanin gona na farin wake guda huɗu da suka haɗa da SAMPEA 22, SAMPEA 23, SAMPEA 24 da kuma SAMPEA 25,” In ji Daraktan.

Ya ƙara da cewa, cibiyar ta kuma fitar da wasu nau’ikan na masara guda biyu, SAMMAZ 78 da kuma na Gyaɗa, SAMNUT 30, tare da ƙarin wasu nau’ikan na Auduga guda huɗu da na masara guda tara, waɗanda aka fitar ta hanyar haɗaka tsakanin ƙungiyar aikin noma ta ƙasa da ƙasa da kuma kamfanonin cikin gida masu sarrafa Irin noma.

Ya kuma yi na’am, kan damar da Gwamnatin Jihar Ribas ta bayar, na amincewa da kafa cibiyar gudanar da binciken aikin noma, domin amfanin ƴan jihar.

Daraktan, ya kuma miƙa ƙoƙon bara ga ɗaukacin gwamnatocin da ke Arewacin ƙasar, da su yi koyi da gwamnatin ta Ribas.

A nasa jawabin, Farfesa Adamu Ahmed, Shugaban Jami’ar ABU, ya buƙaci mahalarta taron bitar da cewa, ba wai kaɗai mayar da hankalai kan samar da wadataccen abinci a ƙasar ba, su tabbata sun lalubo da wasu hanyoyin ingancin abininci, ta hanyar gudanar da bincike wanda hakan zai amfani ɗaukacin al’ummar ƙasar.

Adamu, wanda Mataimakinsa Farfesa Bello Sabo, ya wakilta a wajen taron, ya yi nuni da cewa, za a iya daƙile yunwa da ƙarancin abinci mai gina jiki ne kaɗai a ƙasar, ta hanyar zuba hannun jari a ɓangaren gudanar da bincike.

“Ina mai kira a gare ku, ba wai kaɗai gudanar da bincke ba, domin wallafawa ba, amma akwai matuƙar buƙatar lalubo da mafita kan ragewa ƴan ƙasar matsin tattalin arziƙin da suke ci gaba da fuskanta, ta hanyar yin amfani da fasahar kimiyyar zamani,” a cewar Adamu.

Taken taron bitar shi ne, rage ƙalubalen sauyin yanayin da ke haifar da illa a fannin aikin noma tare da ƙarfafa samar da wadataccen abinci.

Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kashi 30 Kacal Ne Ke Yin Noma Da Kayan Noma Na Zamani A Nijeriya —AFAN

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.