ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

by Abubakar Abba
1 month ago

Cibiyar binciken harkar noma ta Jami’ar Ahamadu Bello da ke Zariya (IAR), na gudanar da ayyukan bincike sama da 140 kan ayyukan noma.

Kazalika, cibiyar ta kuma gabatar da sabbin ayyuka 19, kan kakar aikin noma ta 2026, inda ayyukan suka kai jimillar 159.

Farfesa Ado Yusuf, Daraktan Cibiyar, ya sanar da haka ne yayin taron bita, wanda ya haɗa da na shiyya, wato REFILS, domin yin nazari kan binciken aikin na 2026 da aka saba gudanarwa a duk shekara.

ADVERTISEMENT

Taron, wanda ya gudana a cibiyar da ke jami’ar Ahmadu Bello da ke Samaru a garin na Zariya, Farfesa Nafi’u Abdu Yusuf, Mataimakin Daraktan Cibiyar ne ya wakilci Farfesa Ado Yusuf.

Ya yi nuni da cewa, a ɗaukacin faɗin duniya, ana ci gaba fuskantar ƙalubalen sauyin yanayi, ƙarancin ruwan sama da kuma saurin ɗaukewar ruwan sama.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ya ƙara da cewa, saboda waɗannan matsalolin, akwai buƙatar a gudanar da binciken, domin lalubo da mafita a kan ƙalubalen.

Ya ci gaba da cewa, ayyukan binciken da cibiyar ta gudanar a 2026, cibiyar ta mayar da hankali ne a kan nauyin da aka ɗora mata kan yin binciken amfanin gona da nufin gano nau’ikan amfanin na gona da za su iya jurewa kowane irin yanayi.

A cewarsa, aikin zai taimaka wajen ƙara samarwa da manoman ƙasar nan kuɗaɗen shiga da kuma ƙara haɓaka samar da wadatacccen abinci a ƙasar.

Ya ce, cibiyar shekaru sama da goma da suka gabata, na ci gaba da ksancewa ɗaya tilo a ƙasar, wacce ta ci gaba da fitar da nau’ika amfanin gona ga manoman ƙasar.

“A 2026 kacal, cibiyar ta fitar da nau’ikan amfanin gona na farin wake guda huɗu da suka haɗa da SAMPEA 22, SAMPEA 23, SAMPEA 24 da kuma SAMPEA 25,” In ji Daraktan.

Ya ƙara da cewa, cibiyar ta kuma fitar da wasu nau’ikan na masara guda biyu, SAMMAZ 78 da kuma na Gyaɗa, SAMNUT 30, tare da ƙarin wasu nau’ikan na Auduga guda huɗu da na masara guda tara, waɗanda aka fitar ta hanyar haɗaka tsakanin ƙungiyar aikin noma ta ƙasa da ƙasa da kuma kamfanonin cikin gida masu sarrafa Irin noma.

Ya kuma yi na’am, kan damar da Gwamnatin Jihar Ribas ta bayar, na amincewa da kafa cibiyar gudanar da binciken aikin noma, domin amfanin ƴan jihar.

Daraktan, ya kuma miƙa ƙoƙon bara ga ɗaukacin gwamnatocin da ke Arewacin ƙasar, da su yi koyi da gwamnatin ta Ribas.

A nasa jawabin, Farfesa Adamu Ahmed, Shugaban Jami’ar ABU, ya buƙaci mahalarta taron bitar da cewa, ba wai kaɗai mayar da hankalai kan samar da wadataccen abinci a ƙasar ba, su tabbata sun lalubo da wasu hanyoyin ingancin abininci, ta hanyar gudanar da bincike wanda hakan zai amfani ɗaukacin al’ummar ƙasar.

Adamu, wanda Mataimakinsa Farfesa Bello Sabo, ya wakilta a wajen taron, ya yi nuni da cewa, za a iya daƙile yunwa da ƙarancin abinci mai gina jiki ne kaɗai a ƙasar, ta hanyar zuba hannun jari a ɓangaren gudanar da bincike.

“Ina mai kira a gare ku, ba wai kaɗai gudanar da bincke ba, domin wallafawa ba, amma akwai matuƙar buƙatar lalubo da mafita kan ragewa ƴan ƙasar matsin tattalin arziƙin da suke ci gaba da fuskanta, ta hanyar yin amfani da fasahar kimiyyar zamani,” a cewar Adamu.

Taken taron bitar shi ne, rage ƙalubalen sauyin yanayin da ke haifar da illa a fannin aikin noma tare da ƙarfafa samar da wadataccen abinci.

Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.