Jam’iyyar APC na fuskantar barazanar tawaye daga fusatattun ƴan takara da suka sha kaye a zaɓen fitar da gwani, jam’iyyar mai mulki na fuskantar yiwuwar wata tawaye ta cikin gida da za ta iya lalata mata damar cin nasara a zaɓen 2027.
Barazanar da APC ke fuskanta za a iya kwatanta ta a matsayin wanda za a yi zato ba. An bayyana cewa mafi yawancin fusatattun ƴan takara ba su amince da tsarin zaɓen fid da gwanin ba a ciki jam’iyyar.
A tsakiyar guguwar da ke tasowa akwai wani rukuni na masu neman takara waɗanda suka zuba kuɗaɗe masu yawa, a wasu lokuta, suna kashe miliyoyin naira wajen sayan fom na nuna sha’awar tsayawa takara, sai dai su tsinci kansu an cire su daga katara, an yi watsar da su ko kuma an kayar da su ta hanyoyin da suke ganin ba a yi masu adalci ba.
Abin da ya sa suka shiga wannan yanayi shi ne, wani tarkon doka da suka faɗa ciki ba tare da sun fahimci tasirinsa ba. Dokar zaɓe da aka gyara ƙarƙashin sashe na 77 na dokar zaɓe ta 2026, kowane mutum da ya san yana riƙe da kasancewar mamba na jam’iyyun siyasa biyu a lokaci guda zai rasa matsayin amincewa a matsayin sahihin mamba na kowanne jam’iyya, har sai an daidaita bisa tanadin dokar.
Ga ƴan takara masu amfani da katin mambobin jam’iyyu biyu a baya a matsayin zaɓi na siyasa mai inganci, wannan doka ta rufe ƙofa da ba su sani ba.
Yawancin majiyoyi sun tabbatar da cewa sun fahimci cikakken nauyin wannan takunkumi ne kawai bayan sun riga sun sanya kuɗinsu a cikin tsarin farko. Idan an fuskanci rashin wani zaɓi na siyasa mai yiwuwa, lissafin yawancin waɗannan ƴan takara masu ƙorafi ya canza daga neman arziki a wani waje zuwa neman ramuwar gayya.
Ayyukan cin amanar jam’iyya, wanda shi ne makaman siyasa na cikin gida, sun zama wani mataki na ƙarshe ga waɗanda suka yi rashin nasara kuma suna tunanin ba a yi masu adalci ba.
Girman yawan waɗanda aka soke takararsu na da ban tsoro. Sama da ƴan takara 180 na APC a faɗin ƙasar sun fice daga zaɓukan fid da gwani. Har ila yau, an dakatar da dama daga jam’iyya, saboda haka sun sami kwarin giwar neman haƙƙinsu a kotu kan abin da suka bayyana a matsayin tilasta wa ƴan takara.
A wasu jihohi da dama, akwai hannun gwamnoni wajen tantance sakamako zaɓe. Samfurin amfani da hanyar masalaha, wanda a fili yake a matsayin wata hanya ta samun yarjejeniya cikin tsari, a aikace ya zama kamar hanyar talasta wa ƴan takara, inda manyan jami’an jihar ke amfani da ikonsu na tsarin jam’iyya don zaɓar masu biyayya kuma su gabatar da sakamakon a matsayin an yi amfani da hanyar masalaha a tsakanin ƴan takara.
Shugaban jam’iyyar APC, Nentawe Yilwatda, ya mayar da martani ga barazanar da ke ƙaruwa wanda bai gamsar da kowanne ɓangare na muhawarar ba.
A cikin wata sanarwa na baya-bayan nan da wasu masu lura da jam’iyya suka bayyana a matsayin kamar zuba gishiri a kan rauni, Yilwatda ya yi barazanar ga fusatattun ƴan takara take barazanar tayar da tarzoma ko cin amanar jam’iyya waɗanda za su iya raunana ingancin tsarin zaɓen farko fid da gwani.
“A cikin kowace tsarin dimokuraɗiyya, mutum ɗaya ne kawai zai samu nasara. Abin da ya fi muhimmanci shi ne, ci gaba da aiki tare. Ina ƙarfafa duk masu neman muƙami su nuna dattaku, ƙaunar ƙasa da kyakkyawar zuciya ta hanyar rungumar sakamakon zaɓen fitar da gwani domin amfanin jam’iyya da dimokuraɗiyyarmu gaba ɗaya,” in ji shi.















Discussion about this post