ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

by Yusuf Shuaibu
2 weeks ago

Jam’iyyar APC na fuskantar barazanar tawaye daga fusatattun ƴan takara da suka sha kaye a zaɓen fitar da gwani, jam’iyyar mai mulki na fuskantar yiwuwar wata tawaye ta cikin gida da za ta iya lalata mata damar cin nasara a zaɓen 2027.

Barazanar da APC ke fuskanta za a iya kwatanta ta a matsayin wanda za a yi zato ba. An bayyana cewa mafi yawancin fusatattun ƴan takara ba su amince da tsarin zaɓen fid da gwanin ba a ciki jam’iyyar.

A tsakiyar guguwar da ke tasowa akwai wani rukuni na masu neman takara waɗanda suka zuba kuɗaɗe masu yawa, a wasu lokuta, suna kashe miliyoyin naira wajen sayan fom na nuna sha’awar tsayawa takara, sai dai su tsinci kansu an cire su daga katara, an yi watsar da su ko kuma an kayar da su ta hanyoyin da suke ganin ba a yi masu adalci ba.

ADVERTISEMENT

Abin da ya sa suka shiga wannan yanayi shi ne, wani tarkon doka da suka faɗa ciki ba tare da sun fahimci tasirinsa ba. Dokar zaɓe da aka gyara ƙarƙashin sashe na 77 na dokar zaɓe ta 2026, kowane mutum da ya san yana riƙe da kasancewar mamba na jam’iyyun siyasa biyu a lokaci guda zai rasa matsayin amincewa a matsayin sahihin mamba na kowanne jam’iyya, har sai an daidaita bisa tanadin dokar.

Ga ƴan takara masu amfani da katin mambobin jam’iyyu biyu a baya a matsayin zaɓi na siyasa mai inganci, wannan doka ta rufe ƙofa da ba su sani ba.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Yawancin majiyoyi sun tabbatar da cewa sun fahimci cikakken nauyin wannan takunkumi ne kawai bayan sun riga sun sanya kuɗinsu a cikin tsarin farko. Idan an fuskanci rashin wani zaɓi na siyasa mai yiwuwa, lissafin yawancin waɗannan ƴan takara masu ƙorafi ya canza daga neman arziki a wani waje zuwa neman ramuwar gayya.

Ayyukan cin amanar jam’iyya, wanda shi ne makaman siyasa na cikin gida, sun zama wani mataki na ƙarshe ga waɗanda suka yi rashin nasara kuma suna tunanin ba a yi masu adalci ba.

Girman yawan waɗanda aka soke takararsu na da ban tsoro. Sama da ƴan takara 180 na APC a faɗin ƙasar sun fice daga zaɓukan fid da gwani. Har ila yau, an dakatar da dama daga jam’iyya, saboda haka sun sami kwarin giwar neman haƙƙinsu a kotu kan abin da suka bayyana a matsayin tilasta wa ƴan takara.

A wasu jihohi da dama, akwai hannun gwamnoni wajen tantance sakamako zaɓe. Samfurin amfani da hanyar masalaha, wanda a fili yake a matsayin wata hanya ta samun yarjejeniya cikin tsari, a aikace ya zama kamar hanyar talasta wa ƴan takara, inda manyan jami’an jihar ke amfani da ikonsu na tsarin jam’iyya don zaɓar masu biyayya kuma su gabatar da sakamakon a matsayin an yi amfani da hanyar masalaha a tsakanin ƴan takara.

Shugaban jam’iyyar APC, Nentawe Yilwatda, ya mayar da martani ga barazanar da ke ƙaruwa wanda bai gamsar da kowanne ɓangare na muhawarar ba.

A cikin wata sanarwa na baya-bayan nan da wasu masu lura da jam’iyya suka bayyana a matsayin kamar zuba gishiri a kan rauni, Yilwatda ya yi barazanar ga fusatattun ƴan takara take barazanar tayar da tarzoma ko cin amanar jam’iyya waɗanda za su iya raunana ingancin tsarin zaɓen farko fid da gwani.

“A cikin kowace tsarin dimokuraɗiyya, mutum ɗaya ne kawai zai samu nasara. Abin da ya fi muhimmanci shi ne, ci gaba da aiki tare. Ina ƙarfafa duk masu neman muƙami su nuna dattaku, ƙaunar ƙasa da kyakkyawar zuciya ta hanyar rungumar sakamakon zaɓen fitar da gwani domin amfanin jam’iyya da dimokuraɗiyyarmu gaba ɗaya,” in ji shi.

Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya

Yadda Za Ku Tattala Kuɗaɗen Da Ke Shigowa Hannu Domin Ci Gaban Rayuwa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.