ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

by Yusuf Shuaibu
1 month ago

Jam’iyyar APC na fuskantar barazanar tawaye daga fusatattun ƴan takara da suka sha kaye a zaɓen fitar da gwani, jam’iyyar mai mulki na fuskantar yiwuwar wata tawaye ta cikin gida da za ta iya lalata mata damar cin nasara a zaɓen 2027.

Barazanar da APC ke fuskanta za a iya kwatanta ta a matsayin wanda za a yi zato ba. An bayyana cewa mafi yawancin fusatattun ƴan takara ba su amince da tsarin zaɓen fid da gwanin ba a ciki jam’iyyar.

A tsakiyar guguwar da ke tasowa akwai wani rukuni na masu neman takara waɗanda suka zuba kuɗaɗe masu yawa, a wasu lokuta, suna kashe miliyoyin naira wajen sayan fom na nuna sha’awar tsayawa takara, sai dai su tsinci kansu an cire su daga katara, an yi watsar da su ko kuma an kayar da su ta hanyoyin da suke ganin ba a yi masu adalci ba.

ADVERTISEMENT

Abin da ya sa suka shiga wannan yanayi shi ne, wani tarkon doka da suka faɗa ciki ba tare da sun fahimci tasirinsa ba. Dokar zaɓe da aka gyara ƙarƙashin sashe na 77 na dokar zaɓe ta 2026, kowane mutum da ya san yana riƙe da kasancewar mamba na jam’iyyun siyasa biyu a lokaci guda zai rasa matsayin amincewa a matsayin sahihin mamba na kowanne jam’iyya, har sai an daidaita bisa tanadin dokar.

Ga ƴan takara masu amfani da katin mambobin jam’iyyu biyu a baya a matsayin zaɓi na siyasa mai inganci, wannan doka ta rufe ƙofa da ba su sani ba.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Yawancin majiyoyi sun tabbatar da cewa sun fahimci cikakken nauyin wannan takunkumi ne kawai bayan sun riga sun sanya kuɗinsu a cikin tsarin farko. Idan an fuskanci rashin wani zaɓi na siyasa mai yiwuwa, lissafin yawancin waɗannan ƴan takara masu ƙorafi ya canza daga neman arziki a wani waje zuwa neman ramuwar gayya.

Ayyukan cin amanar jam’iyya, wanda shi ne makaman siyasa na cikin gida, sun zama wani mataki na ƙarshe ga waɗanda suka yi rashin nasara kuma suna tunanin ba a yi masu adalci ba.

Girman yawan waɗanda aka soke takararsu na da ban tsoro. Sama da ƴan takara 180 na APC a faɗin ƙasar sun fice daga zaɓukan fid da gwani. Har ila yau, an dakatar da dama daga jam’iyya, saboda haka sun sami kwarin giwar neman haƙƙinsu a kotu kan abin da suka bayyana a matsayin tilasta wa ƴan takara.

A wasu jihohi da dama, akwai hannun gwamnoni wajen tantance sakamako zaɓe. Samfurin amfani da hanyar masalaha, wanda a fili yake a matsayin wata hanya ta samun yarjejeniya cikin tsari, a aikace ya zama kamar hanyar talasta wa ƴan takara, inda manyan jami’an jihar ke amfani da ikonsu na tsarin jam’iyya don zaɓar masu biyayya kuma su gabatar da sakamakon a matsayin an yi amfani da hanyar masalaha a tsakanin ƴan takara.

Shugaban jam’iyyar APC, Nentawe Yilwatda, ya mayar da martani ga barazanar da ke ƙaruwa wanda bai gamsar da kowanne ɓangare na muhawarar ba.

A cikin wata sanarwa na baya-bayan nan da wasu masu lura da jam’iyya suka bayyana a matsayin kamar zuba gishiri a kan rauni, Yilwatda ya yi barazanar ga fusatattun ƴan takara take barazanar tayar da tarzoma ko cin amanar jam’iyya waɗanda za su iya raunana ingancin tsarin zaɓen farko fid da gwani.

“A cikin kowace tsarin dimokuraɗiyya, mutum ɗaya ne kawai zai samu nasara. Abin da ya fi muhimmanci shi ne, ci gaba da aiki tare. Ina ƙarfafa duk masu neman muƙami su nuna dattaku, ƙaunar ƙasa da kyakkyawar zuciya ta hanyar rungumar sakamakon zaɓen fitar da gwani domin amfanin jam’iyya da dimokuraɗiyyarmu gaba ɗaya,” in ji shi.

Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya

Yadda Za Ku Tattala Kuɗaɗen Da Ke Shigowa Hannu Domin Ci Gaban Rayuwa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026
'Yan Bindiga

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.