ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cutar Sikila Ba Mutuwa Ba Ce – Ƙwararru

by Sani Anwar and Sulaiman
7 months ago
Sikila

Ƙwararru a harkar kiwon lafiya sun bayyana cewa, cutar Sikila ko kadan ba tana nuna alamun mutuwa ba ce. Sun bayyana hakan ne, a wani taro da aka gudanar a Abuja; wanda ake kokarin sauya tunanin mutane a kan wannan cuta tare kuma da yin bikin ranar Sikila ta duniya.

Kungiyar ‘Mirror Me’ tare da hadin gwiwar ‘Gehenesphere’ ne suka shirya taron, wanda ya bayar da haske a kan makomar Kobiro Es- elemo, fitacce kuma jigo a cikin al’ummar da ke dauke da wannan cuta ta Sikila.

  • ‘Yansanda Sun Ƙaryata Shirin Kai Harin Ta’addanci Jihar Kogi
  • Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka

Babban jami’i na kungiyar ta ‘Mir- ror Me’ da mashiryin taron, Daniel Ojo, sun jaddada bukatar canzawar tunanin al’umma dangane da wannan cuta ta Sikila.

ADVERTISEMENT

“Cutar Sikila, ko kadan ba ta daukar hukuncin kisa ko wani abu mai kama da haka”, kamar yadda Ojo ya bayyana. Haka zalika, wajibi ne, mu daina kallon masu dauke da wannan cuta a matsayin raunana ko kasassu a cikin mutane, domin kuwa suna da karfi da kuma juriya irin nasu, sannan lokaci ya yi da al’umma za ta gane tare da fahimtar hakan”, in ji shi.

Olunaike, babban mai jawabi a wajen taron; ta goyi bayan wannan furuci na Ojo, inda ta jaddada muhimmancin nuna halayya mai kyau da kuma bukatar tallafa wa al’ummar da ke dauke da wannan cuta ta Sikila. Sannan, ta bukaci ma’aikatan kiwon lafiya da su kasance masu tausayi da jin kai da tausasawa tare kuma da nuna taka-tsantsan wajen amfani da miyagun kwayoyi a tsakanin marasa lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

“Dole ne mu kawar da tatsuniyar cewa, masu dauke da wannan cuta ta Sikila na shan wahala wajen shan magungunansu, ko shakka babu, wannan kawai wani shaci fadi ne da mutane suka jima suna shata suna fada.

“Sannan, masu daukar ma’aikata, su ma dole ne su cire son zuciya da son rai wajen daukar masu cutar Sikila aiki. Domin kuwa ko shakka babu, wadannan bayin Allah na da dama tare da ‘yanci da kuma kwarewa kamar kowa da kowa a fadin wannan kasa”, in ji Olunaike.

Da yake yin nasa karin hasken, Obye Ewuge kwararren likitan jini a cibiyar kiwon lafiya ta tarayya da ke Keffi ta Jihar Nassarawa, ya jaddada yadda za a magance kamuwa da cutar da kuma kula da masu ita yadda ya dace.

Haka zalika, ya sake Bljaddada muhimmancin neman kulawar likita, lokacin da ake cikin tsanani da tashin hankali; maimakon dogaro da magunguna kadai.

Har ila yau, cutar Sikila ba mutuwa ba ce; domin kuwa masu dauke da cutar, su ma mutane ne kamar kowa da ke da kima, ilimi, hazaka, basira da mutuntaka a tsakanin al’umma, don haka, wajibi ne a mutunta su tare da ba su dukkanin gudunmawar da ta kamata.

Sikila
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnati Ta Amince Da Inganta Cibiyar Kula Da Saran Maciji A Gwambe
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Hukumar NDLEA Ta Lalata Sama Da Tan 12 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
Sikila
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • Sulaiman
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
  • Sulaiman
    Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

MASU ALAKA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
Kiwon Lafiya

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

June 20, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
Kiwon Lafiya

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir
Kiwon Lafiya

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

May 30, 2026
Next Post
Layin Dogon Da Zai Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanantar Da Kansu

Layin Dogon Da Zai Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanantar Da Kansu

LABARAI MASU NASABA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.