ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cutar Sikila Ba Mutuwa Ba Ce – Ƙwararru

by Sani Anwar and Sulaiman
8 months ago
Sikila

Ƙwararru a harkar kiwon lafiya sun bayyana cewa, cutar Sikila ko kadan ba tana nuna alamun mutuwa ba ce. Sun bayyana hakan ne, a wani taro da aka gudanar a Abuja; wanda ake kokarin sauya tunanin mutane a kan wannan cuta tare kuma da yin bikin ranar Sikila ta duniya.

Kungiyar ‘Mirror Me’ tare da hadin gwiwar ‘Gehenesphere’ ne suka shirya taron, wanda ya bayar da haske a kan makomar Kobiro Es- elemo, fitacce kuma jigo a cikin al’ummar da ke dauke da wannan cuta ta Sikila.

  • ‘Yansanda Sun Ƙaryata Shirin Kai Harin Ta’addanci Jihar Kogi
  • Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka

Babban jami’i na kungiyar ta ‘Mir- ror Me’ da mashiryin taron, Daniel Ojo, sun jaddada bukatar canzawar tunanin al’umma dangane da wannan cuta ta Sikila.

ADVERTISEMENT

“Cutar Sikila, ko kadan ba ta daukar hukuncin kisa ko wani abu mai kama da haka”, kamar yadda Ojo ya bayyana. Haka zalika, wajibi ne, mu daina kallon masu dauke da wannan cuta a matsayin raunana ko kasassu a cikin mutane, domin kuwa suna da karfi da kuma juriya irin nasu, sannan lokaci ya yi da al’umma za ta gane tare da fahimtar hakan”, in ji shi.

Olunaike, babban mai jawabi a wajen taron; ta goyi bayan wannan furuci na Ojo, inda ta jaddada muhimmancin nuna halayya mai kyau da kuma bukatar tallafa wa al’ummar da ke dauke da wannan cuta ta Sikila. Sannan, ta bukaci ma’aikatan kiwon lafiya da su kasance masu tausayi da jin kai da tausasawa tare kuma da nuna taka-tsantsan wajen amfani da miyagun kwayoyi a tsakanin marasa lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta

“Dole ne mu kawar da tatsuniyar cewa, masu dauke da wannan cuta ta Sikila na shan wahala wajen shan magungunansu, ko shakka babu, wannan kawai wani shaci fadi ne da mutane suka jima suna shata suna fada.

“Sannan, masu daukar ma’aikata, su ma dole ne su cire son zuciya da son rai wajen daukar masu cutar Sikila aiki. Domin kuwa ko shakka babu, wadannan bayin Allah na da dama tare da ‘yanci da kuma kwarewa kamar kowa da kowa a fadin wannan kasa”, in ji Olunaike.

Da yake yin nasa karin hasken, Obye Ewuge kwararren likitan jini a cibiyar kiwon lafiya ta tarayya da ke Keffi ta Jihar Nassarawa, ya jaddada yadda za a magance kamuwa da cutar da kuma kula da masu ita yadda ya dace.

Haka zalika, ya sake Bljaddada muhimmancin neman kulawar likita, lokacin da ake cikin tsanani da tashin hankali; maimakon dogaro da magunguna kadai.

Har ila yau, cutar Sikila ba mutuwa ba ce; domin kuwa masu dauke da cutar, su ma mutane ne kamar kowa da ke da kima, ilimi, hazaka, basira da mutuntaka a tsakanin al’umma, don haka, wajibi ne a mutunta su tare da ba su dukkanin gudunmawar da ta kamata.

Sikila
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
Sikila
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka
  • Sulaiman
    Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

MASU ALAKA

Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam
Kiwon Lafiya

Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam

July 25, 2026
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta
Kiwon Lafiya

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Kiwon Lafiya

Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina

July 11, 2026
Next Post
Layin Dogon Da Zai Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanantar Da Kansu

Layin Dogon Da Zai Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanantar Da Kansu

LABARAI MASU NASABA

Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

July 27, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Sikila

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Sikila

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.