ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Layin Dogon Da Zai Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanantar Da Kansu

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Layin dogo

Kwanan nan, an kaddamar da aikin farfado da layin dogo tsakanin Tanzaniya da Zambiya, matakin da zai samar da kuzari ga layin dogon.

Layin dogo dake tsakanin Tanzaniya da Zambiya yana da tsawon kilomita 1860, wanda ya tashi daga tashar ruwa ta Dar es Salaam da ke Tanzania, sa’an nan ya ratsa tudun Tanzania har zuwa Kapiri Mposhi da ke tsakiyar kasar Zambiya, wanda ya taimaka ga hada dimbin kasashe masu arzikin albarkatun kasa da sauran sassan duniya. Kasar Sin ce ta bayar da gudummawar gina wannan layin dogon a kimanin shekarun 1970, don mara baya ga kasashen Tanzania da Zambiya wadanda suka samu ‘yancin kansu daga Turawa ’yan mulkin mallaka, wajen tsayawa da kafafuwansu a fannin tattalin arziki. A shekarar 1976, aka fara aiki da layin dogon, wanda ya samar da wata hanyar zuwa teku ga Zambiya da sauran wasu kasashen shiyyar da ba su da iyaka da teku, ta yadda albarkatun kasashen za su zama karfin bunkasa tattalin arzikinsu, matakin da ya sa kasashen suka yi watsi da tarnakin da aka yi musu ta fannin tattalin arziki tare da samun ‘yanci na gaske. Don haka, tsohon shugaban kasar Zambiya, marigayi Kenneth David Kaunda ya bayyana layin dogon a matsayin “’yancin kan Zambia a karo na biyu”.

A cikin kimanin shekaru 50 da suka wuce, layin dogon ya taka rawar gani wurin bunkasa tattalin arziki da zaman al’umma na Tanzaniya da Zambiya da ma sauran kasashen shiyyar. Sai dai layin dogon yana kuma fuskantar matsalar lalacewa sakamakon dadewarsa da aiki. Don haka, ana matukar bukatar inganta layin dogon don ci gaba da bunkasa tattalin arziki da zaman al’ummar shiyyar. A sabili da haka ne, a gun taron kolin dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka da ya gudana a watan Satumban bara, shugabannin kasashen Sin da Tanzaniya da Zambiya suka rattaba hannu a kan takardar fahimtar juna game da farfado da layin dogo tsakanin Tanzaniya da Zambiya, inda suka amince da dora nauyin aikin a wuyan kasar Sin. An ce, bayan inganta layin dogon, za a kai ga ninka karfin sa na zirga-zirga har sau 12, a yayin da tsawon lokacin zirga-zirga zai ragu da kimanin kaso 2/3, wanda hakan tabbas zai sa kaimi ga bunkasar tattalin arzikin sassan da layin dogon ya ratsa.

ADVERTISEMENT

A hakika, layin dogo tsakanin Tanzaniya da Zambiya wani misali ne na hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka a fannin raya ababen more rayuwa. Ta la’akari da layin dogon dake tsakanin Mombasa da Nairobi da wanda ke tsakanin Abuja da Kaduna, da tashar samar da wutar lantarki ta karfin iska da ke garin De Aar na kasar Afirka ta Kudu da tashar samar da lantarki ta karfin ruwa ta Zungeru da ke Nijeriya, da ma sauran ababen more rayuwa da ba sa lisaftuwa da kamfanonin kasar Sin suka gina, za mu gano cewa, a cikin ’yan shekarun baya, kasar Sin ta gina jerin layukan dogo da hanyoyi da tashoshin ruwa da tashoshin samar da lantarki da asibitoci a wurare daban daban na nahiyar Afirka, wadanda suka kyautata tushen bunkasuwar tattalin arzikin nahiyar, tare da sa kaimi ga bunkasuwar masana’antu da zamanantar da kasashen Afirka.

Amma me ya sa kasar Sin ke iyakacin kokari wajen taimakawa kasashen Afirka raya ababen more rayuwa? Lallai a ganina, hakan ya faru ne sakamakon dadadden zumuncin dake tsakaninsu, da burinsu na neman tabbatar da moriyar juna, da ma yadda kasar Sin ke rungumar manufar gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Bisa ga yadda ta cimma nasarori ta fuskar samun ci gaban tattalin arziki, kasar Sin tana sane da cewa, manyan ababen more rayuwa su ne tushen bunkasuwar tattalin arziki da zamantakewar al’umma, don haka ta gabatar da dabarunta ga kasashen Afirka, don inganta tushen bunkasa masana’antu a kasashen, da ma kwarewarsu ta raya kansu.

A sa’i daya, Sin da kasashen Afirka suna amfanin juna bisa hadin gwiwarsu ta gina ababen more rayuwa. Kasashen Afirka suna da yawan matasa da albarkatun kasa da ma manyan kasuwanni, sai dai dole ne su kyautata ababen more rayuwa don fifikonsu a fannonin ya taka rawar da ta kamata. Kasar Sin a nata bangaren, tana da fifiko ta fannonin kera na’urori da gine-gine da ma tara kudade, wanda hakan ke iya tallafa wa kasashen Afirka, kuma a wani bangare, hakan na iya samar da sabbin kasuwanni ga kamfanonin kasar Sin, ta yadda sassan biyu za su iya samun ci gaba na bai daya.

Ban da haka, a yayin da ake fuskantar matsalar rashin daidaiton bunkasuwar kasashen duniya, kasar Sin tana kokarin hada gwiwa da kasashen Afirka wajen gina ababen more rayuwa, domin aiwatar da manufarta ta gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkanin bil Adam, sabo da farfadowar nahiyar Afirka ba alhairan da za su shafi al’ummar nahiyar kawai za ta samar ba, har ma da taimakawa wajen kafa tsarin kasa da kasa mai adalci da daidaito. (Lubabatu Lei)

 

Layin dogo
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri
Layin dogo
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Morocco: Kasar Da Ke Neman Zama Fuskar Kwallon Ƙafa A Duniya

Morocco: Kasar Da Ke Neman Zama Fuskar Kwallon Ƙafa A Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

June 28, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

June 28, 2026
Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

June 28, 2026
Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

June 28, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

El-Rufai Ya Shafe Fiye Da Kwanaki 125 A Garƙame

June 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.