ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Layin Dogon Da Zai Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanantar Da Kansu

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
Layin dogo

Kwanan nan, an kaddamar da aikin farfado da layin dogo tsakanin Tanzaniya da Zambiya, matakin da zai samar da kuzari ga layin dogon.

Layin dogo dake tsakanin Tanzaniya da Zambiya yana da tsawon kilomita 1860, wanda ya tashi daga tashar ruwa ta Dar es Salaam da ke Tanzania, sa’an nan ya ratsa tudun Tanzania har zuwa Kapiri Mposhi da ke tsakiyar kasar Zambiya, wanda ya taimaka ga hada dimbin kasashe masu arzikin albarkatun kasa da sauran sassan duniya. Kasar Sin ce ta bayar da gudummawar gina wannan layin dogon a kimanin shekarun 1970, don mara baya ga kasashen Tanzania da Zambiya wadanda suka samu ‘yancin kansu daga Turawa ’yan mulkin mallaka, wajen tsayawa da kafafuwansu a fannin tattalin arziki. A shekarar 1976, aka fara aiki da layin dogon, wanda ya samar da wata hanyar zuwa teku ga Zambiya da sauran wasu kasashen shiyyar da ba su da iyaka da teku, ta yadda albarkatun kasashen za su zama karfin bunkasa tattalin arzikinsu, matakin da ya sa kasashen suka yi watsi da tarnakin da aka yi musu ta fannin tattalin arziki tare da samun ‘yanci na gaske. Don haka, tsohon shugaban kasar Zambiya, marigayi Kenneth David Kaunda ya bayyana layin dogon a matsayin “’yancin kan Zambia a karo na biyu”.

A cikin kimanin shekaru 50 da suka wuce, layin dogon ya taka rawar gani wurin bunkasa tattalin arziki da zaman al’umma na Tanzaniya da Zambiya da ma sauran kasashen shiyyar. Sai dai layin dogon yana kuma fuskantar matsalar lalacewa sakamakon dadewarsa da aiki. Don haka, ana matukar bukatar inganta layin dogon don ci gaba da bunkasa tattalin arziki da zaman al’ummar shiyyar. A sabili da haka ne, a gun taron kolin dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka da ya gudana a watan Satumban bara, shugabannin kasashen Sin da Tanzaniya da Zambiya suka rattaba hannu a kan takardar fahimtar juna game da farfado da layin dogo tsakanin Tanzaniya da Zambiya, inda suka amince da dora nauyin aikin a wuyan kasar Sin. An ce, bayan inganta layin dogon, za a kai ga ninka karfin sa na zirga-zirga har sau 12, a yayin da tsawon lokacin zirga-zirga zai ragu da kimanin kaso 2/3, wanda hakan tabbas zai sa kaimi ga bunkasar tattalin arzikin sassan da layin dogon ya ratsa.

ADVERTISEMENT

A hakika, layin dogo tsakanin Tanzaniya da Zambiya wani misali ne na hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka a fannin raya ababen more rayuwa. Ta la’akari da layin dogon dake tsakanin Mombasa da Nairobi da wanda ke tsakanin Abuja da Kaduna, da tashar samar da wutar lantarki ta karfin iska da ke garin De Aar na kasar Afirka ta Kudu da tashar samar da lantarki ta karfin ruwa ta Zungeru da ke Nijeriya, da ma sauran ababen more rayuwa da ba sa lisaftuwa da kamfanonin kasar Sin suka gina, za mu gano cewa, a cikin ’yan shekarun baya, kasar Sin ta gina jerin layukan dogo da hanyoyi da tashoshin ruwa da tashoshin samar da lantarki da asibitoci a wurare daban daban na nahiyar Afirka, wadanda suka kyautata tushen bunkasuwar tattalin arzikin nahiyar, tare da sa kaimi ga bunkasuwar masana’antu da zamanantar da kasashen Afirka.

Amma me ya sa kasar Sin ke iyakacin kokari wajen taimakawa kasashen Afirka raya ababen more rayuwa? Lallai a ganina, hakan ya faru ne sakamakon dadadden zumuncin dake tsakaninsu, da burinsu na neman tabbatar da moriyar juna, da ma yadda kasar Sin ke rungumar manufar gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya.

LABARAI MASU NASABA

An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

Bisa ga yadda ta cimma nasarori ta fuskar samun ci gaban tattalin arziki, kasar Sin tana sane da cewa, manyan ababen more rayuwa su ne tushen bunkasuwar tattalin arziki da zamantakewar al’umma, don haka ta gabatar da dabarunta ga kasashen Afirka, don inganta tushen bunkasa masana’antu a kasashen, da ma kwarewarsu ta raya kansu.

A sa’i daya, Sin da kasashen Afirka suna amfanin juna bisa hadin gwiwarsu ta gina ababen more rayuwa. Kasashen Afirka suna da yawan matasa da albarkatun kasa da ma manyan kasuwanni, sai dai dole ne su kyautata ababen more rayuwa don fifikonsu a fannonin ya taka rawar da ta kamata. Kasar Sin a nata bangaren, tana da fifiko ta fannonin kera na’urori da gine-gine da ma tara kudade, wanda hakan ke iya tallafa wa kasashen Afirka, kuma a wani bangare, hakan na iya samar da sabbin kasuwanni ga kamfanonin kasar Sin, ta yadda sassan biyu za su iya samun ci gaba na bai daya.

Ban da haka, a yayin da ake fuskantar matsalar rashin daidaiton bunkasuwar kasashen duniya, kasar Sin tana kokarin hada gwiwa da kasashen Afirka wajen gina ababen more rayuwa, domin aiwatar da manufarta ta gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkanin bil Adam, sabo da farfadowar nahiyar Afirka ba alhairan da za su shafi al’ummar nahiyar kawai za ta samar ba, har ma da taimakawa wajen kafa tsarin kasa da kasa mai adalci da daidaito. (Lubabatu Lei)

 

Layin dogo
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu
Layin dogo
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Rajistar Shirin Auren Gata Na Kano Kyauta Ce, In Ji Hukumar Hisbah
  • Sulaiman
    An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”
  • Sulaiman
    Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa
  • Sulaiman
    Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

MASU ALAKA

An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”
Ra'ayi Riga

An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”

July 22, 2026
Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?
Ra'ayi Riga

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

July 20, 2026
Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI
Ra'ayi Riga

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

July 19, 2026
Next Post
Morocco: Kasar Da Ke Neman Zama Fuskar Kwallon Ƙafa A Duniya

Morocco: Kasar Da Ke Neman Zama Fuskar Kwallon Ƙafa A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Hisbah

Rajistar Shirin Auren Gata Na Kano Kyauta Ce, In Ji Hukumar Hisbah

July 22, 2026
An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”

An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”

July 22, 2026
Sojoji Sun Daƙile ‘Yan Ta’adda Daga Karɓar Haraji A Yobe

Sojoji Sun Daƙile ‘Yan Ta’adda Daga Karɓar Haraji A Yobe

July 22, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara, Katsina Da Kebbi

July 22, 2026
NNPP Ta Yi Barazanar Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Bin Umarnin Dawo Da Tambarinta A Kan Lokaci

NNPP Ta Yi Barazanar Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Bin Umarnin Dawo Da Tambarinta A Kan Lokaci

July 22, 2026
Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Shugaban Laliga Ya Buƙaci Infantino Ya Sauka Daga Shugabancin FIFA

Shugaban Laliga Ya Buƙaci Infantino Ya Sauka Daga Shugabancin FIFA

July 22, 2026
Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

July 21, 2026
Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

July 21, 2026
Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.