ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dabarun Noman  Kankana A Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
Kankana

Shuka Kankana da girbinta, na kai wa kimanin watanni uku; sannan za ka iya shuka ta tare da girbe ta sau akalla hudu a shekara a kuma Fuloti guda, har ila yau za ka iya shuka sama da 1,596.

A yanzu haka, Kasar Chana ce ke kan gaba a fadin duniya wajen noman Kankana, haka nan kuma wani fanni ne da ke samar da kudaden shiga ga wadanda suka rungumi noman a matsayin sana’a, sannan a Nijeriya za ka iya fara wannan noma da Naira 50,000, banda kudin hayar gona.

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Kashe Naira Biliyan Ɗaya Don Aikin Kiwon Lafiya Kyauta Ga Marasa Ƙarfi A Jihar
  • Da Ɗumi-ɗumi: Bayan CBN, FAAN, Manyan Ma’aikatun Hukumar Man Fetur Na Shirin Komawa Legas

Har ila yau, wanda ya noma fuloti daya; zai iya samun ribar akalla Naira 400,000 a shekara daya kacal, sannan ta na kuma jurewa kowane irin yanayi tare da bijere wa cututtukan da ke harbin amfanin gona.

ADVERTISEMENT

Tsara Yin Kasuwancinta:

Da farko, idan har ba ka tsara yadda za ka yi kasuwancinta ba, tabbas za ka iya tabka asara mai yawan gaske.

LABARAI MASU NASABA

Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

Kazalika, tsarin kasuwancin nata ya hada da aiwatar da kasafin kudin da za ka kashe wajen yin nomanta, inda hakan zai taimaka wa manomin nata wajen samun kudaden shiga masu yawa.

Zabar Ingantaccen Irin Nomanta:

Wannan na daya daga cikin muhimman abubuwan da masu nomanta ya kamata su yi la’akari da shi, musamman a nan Nijeriya, domin kuwa akwai Iri kala-kala; ya danganta da wanda ka ke bukata ka shuka.

Zabo Wajen Shuka Irin:

Shi ma wannan na da matukar muhimmancin gaske duk da cewa, Allah ya albarkaci jihohin kasar nan 36, ciki har da Babban Birnin Tarayyar Abuja da kasar noma.

Sharar Gona:

Mataki na karhe shi ne, sharar gona don shuka Irin Kankana, inda wannnan matakin ya kunshi nome ciyawa, zuba takin gargajiya ko na zamani.

Tsarin Yadda Ake Shuka Irinta:

Wannan ya kunshi yadda ake shuka Iri na Kankana da kuma gyaran gonar da za a shuka Irin, sannan ana so a shuka Irin ta hanyar yin nesa da juna.

Yin Ban Ruwa:

Wajibi ne a tabbatar da an yi ban ruwa yadda ya kamata akalla sau biyu a duk mako, musamman ganin cewa; ta na daya daga cikin amfanin gonar da ke bukatar a yi mata ban ruwa a lokacin da aka shuka ta.

Kare Ta Daga Harbin Kwari Tare Da Nome Ta:

Dole ne a tabbar ana nome mata ciyawa tare da yi mata feshi, domin ba ta kariya daga kamuwa da cututtukan da ke harbin amfanin gona.

Tsarin Yi Mata Girbi:

A nan bayan ‘ya’yan sun girma, sun kai munzalin cirewa; sai a cire su musamman ginin cewa, ta na kai wa daga kimanin kwana 75 zuwa 90 kafin ta nuna.

Adana Ta Bayan Girbi:

Ya na da kyau bayan ka girbe ta, ka tanadi guri mai kyau da za ka adana ta kafin ka kai ta kasuwa, don sayarwa ko kuma samo wanda zai saya, don haka za ka iya adana ta har zuwa tsawon wata daya ba tare da ta yi komai ba, amma kar ka bari ya kasance rana na dukan ta.

Sayarwa:

Za ka iya sayar da Kankanarka baki-daya a lokaci guda, musamman ga manyan shaguna, kasuwanni, kamfanoni ko ga dai-daikun mutane ko kuma ga masu safararta zuwa kasashen waje da sauran makamantansu.

Kankana
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

MASU ALAKA

Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
Noma Da Kiwo

Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

June 6, 2026
Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya
Noma Da Kiwo

Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

June 6, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Next Post
Tsawon Shekaru Nawa Tattabaru Ke Yi A Duniya

Tsawon Shekaru Nawa Tattabaru Ke Yi A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026
Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.