ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dakatar Da Shigo Da Kayan Abinci Zai Iya Haifar Da Yunwa A 2025

by Abubakar Abba
1 year ago
Yunwa

Iyalai da dama na ci gaba da kai mari su kai gwauro, wajen kokarin samun damar yadda za su ciyar da iyalansu sau biyu ko sau uku a rana, wanda hakan ya zo daidai da gazawar gwamnatin kasar na cika alkawarorin da ta yi a 2024, na bayar da damar shigo da kayan abinci kasar.

“Na yi tsammanin tun a 2024, za a fara shigo da kayan abinci cikin kasar nan, amma hakan bai yiwu ba; yanzu haka ina batar da kashi 65 cikin 100 na abin da nake samu, wajen saya wa iyalina abinci; inda sauran kudin kuma ke tafiya a harkokin sufuri da sayen sauran kayan bukatun yau da kullum”, in ji wani magidanci mazaunin Jihar Legas, Ibrahim Wahab.

  • Bajintar Aiki: Majalisar Dattawa Ta Jinjina Wa Ministan Yaɗa Labarai
  • Arsenal Ta Matsawa Liverpool Ƙaimi Bayan Doke Tottenham A Emirates 

“Babu wani sauran kudi da ke raguwa a hannuna da za su ishe ni na zuba hannun jari”, a cewar Wahab.

ADVERTISEMENT

Umarnin gwamnatin tarayya na bari a shigo da kayan abinci daga ketare, na kunshe ne cikin wata wasika mai dauke da kwanan watan Yulin 2024, wanda ma’ikatar kudi ta fitar.

Ma’ikatar kudin, ta yi bayani kan dakatar da shirin bayar da damar shigo da kayan abinci cikin kasar da suka hada da; Shinkafa, Alkama, Masara da kuma wasu sauran kayan abincin.

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

Har ila yau, gwamnatin ta yi yunkurin bayar da damar shigo da kayan abincin ne, domin saukaka tsadar kayan abincin a Nijeriya.

Kudin fiton kayan abincin da suka hada da Shinkafa, Dawa da kuma Wake, ya kai daga kashi 5 zuwa kashi 30.

An Dora Alhakin Rashin Bayar Da Damar Shigo Da Kayan Abincin Kan Ma’aikatar Kudi:

Mai magana da yawun Hukumar Hana Fasakwuri ta Kasa, Abdullahi Maiwada; a makon da ya gabata, ya dora alhakin rashin bayar da damar shigo da kayan abincin a kan ma’aikatar kudi.

Maiwada, a hirarsa da jaridar BusinessDay a watan Satumbar 2024, ya dora laifin a kan ma’aikatar kudin; kan jinkirin wanzar da damar barin shigo da kayan abincin cikin kasar.

A cewarsa, ma’aikatar ta gaza mika jerin sunayen masu shigo da kayan da kuma sauran kamfanonin da suka cika sharuddan shigo da kayan abincin kamar yadda aka tsara.

“Kamar yadda Hukumar Kwastan ta Kasa, ta isar da tsare-tsaren shigo da kayan abincin; da ma’aikatar kudin ta amincewa tar da bayar da dama, da tuni an fara wanzar da shirin bayar da umarnin shigo da kayan”, in ji Maiwada.

Ya ci gaba da cewa, “Amma tun bayan da tsarin barin shigo da kayan ya fito daga ma’aikatar kudin, ya kamata a ce ta bayar da jerin sunayen wadanda suka cancanta su shigo da kayan”.

Wani bincike da jaridar ta BusinessDay ta gudanar ya nuna cewa, har zuwa watan Disambar 2024, ma’aikatar kudin ba ta tura wa Hukumar Kwastan jerin sunayen masu shigo da kayan ba; sannan kuma ba ta yi wani gamsasshen bayani ba.

Ci Gaba Da Fuskantar Barazanar Yunwa A Kasar:

Fiye da mutum 67 ne, ciki har da kanannan yara suka rasa rayukansu a turmutsutsun rabon kayan abinci a Nijeriya, daidai lokacin shagulgulan bikin karshen shekarar 2024; a wasu sassan kasar.

Wasu masu fashin baki kan al’amuran yau da kullum sun bayyana cewa, lamarin ya nuna a zahiri irin matsananciyar yunwar da talakawan kasar ke ci gaba da fuskanta.

Shirin samar da abinci na Majalisar Dinkin Duniya (WFP) a farkon shekarar 2024 ya bayyana cewa, ‘yan Nijeriya miliyan 33 ne za su fuskanci yunwa a 2025, ban da kuma wasu daga cikin ‘yan kasar kimanin miliyan 25 da suka fuskanci yunwar a 2024.

Mai magana da yawun shirin na WFP, Chi Lael; ya sheda wa manema labarai a taron Geneba na 2024 cewa, ‘yan Nijeriya da dama; abincin da za su ci ya gagare su.

Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu, ta kirkiro da tsauraran matakai na bunkasa tattalin arzikin kasar, ciki har da cire tallafin mai da sauran makamantansu cikin daukacin fadin kasar.

A watan Nuwambar da ya gabata, an samu hauhawar farashin kayayyaki da kashi 34.6, da ya haura wanda aka taba samu cikin shekaru 28 a kasar, inda farashin kayan abinci ya karu da kashi 39.9 a shekarar 2024.

Wani rahoton girke-girke da aka fitar ya nuna cewa, a watan Satumbar 2024, magidanci mai ‘ya’ya biyar, na kashe akalla 21,300 cikin wata hudu idan zai dafa hadaddiyar Shinkafa, inda hakan ya karu da kashi 5.1 cikin 100.

A yanzu haka, ana sayar da buhun Shinkafa mai nauyin kilo 50; wacce ake shigo da ita daga waje da kuma wadda ake nomawa a kasar, kan Naira 100,000, inda farashinsu ya dara sabon mafi karancin albashin ma’aikata na Naira 70,000.

Bugu da kari, farashin kayan abinci da suka hada da Wake, Rogo, Dankali da sauransu, sun yi tashin gwauron zabi da kashi 100 cikin shekara daya tare kuma da kalubalen rashin tsaro da ya kara haddasa hakan.

Wani mai suna Daniel Brown, a fannin shigo da kaya cikin kasar ya bayyana cewa, “Tsadar kayan abinci ta karu a kasar, sakamakon rashin aiwatar da tsarin da gwamnatin ta gaza yi a watan Julin  2024”.

“Sai dai, rashin wanzar da wannan tsari; ya nuna a zahiri gazawar hukumomin gwamnatin taraya, wanda hakan ya kara jefa rayuwar talakawan kasar cikin wata matsalar daban”, in ji Brown.

Yunwa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

MASU ALAKA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 
Noma Da Kiwo

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
Next Post
Dalilin Rahoton Farfesa Jega Na Bukatar Taimaka Wa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona

Dalilin Rahoton Farfesa Jega Na Bukatar Taimaka Wa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

July 10, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

July 10, 2026
CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

July 10, 2026
Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

July 10, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?

July 10, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.