ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dakatar Da Shigo Da Kayan Abinci Zai Iya Haifar Da Yunwa A 2025

by Abubakar Abba
2 years ago
Yunwa

Iyalai da dama na ci gaba da kai mari su kai gwauro, wajen kokarin samun damar yadda za su ciyar da iyalansu sau biyu ko sau uku a rana, wanda hakan ya zo daidai da gazawar gwamnatin kasar na cika alkawarorin da ta yi a 2024, na bayar da damar shigo da kayan abinci kasar.

“Na yi tsammanin tun a 2024, za a fara shigo da kayan abinci cikin kasar nan, amma hakan bai yiwu ba; yanzu haka ina batar da kashi 65 cikin 100 na abin da nake samu, wajen saya wa iyalina abinci; inda sauran kudin kuma ke tafiya a harkokin sufuri da sayen sauran kayan bukatun yau da kullum”, in ji wani magidanci mazaunin Jihar Legas, Ibrahim Wahab.

  • Bajintar Aiki: Majalisar Dattawa Ta Jinjina Wa Ministan Yaɗa Labarai
  • Arsenal Ta Matsawa Liverpool Ƙaimi Bayan Doke Tottenham A Emirates 

“Babu wani sauran kudi da ke raguwa a hannuna da za su ishe ni na zuba hannun jari”, a cewar Wahab.

ADVERTISEMENT

Umarnin gwamnatin tarayya na bari a shigo da kayan abinci daga ketare, na kunshe ne cikin wata wasika mai dauke da kwanan watan Yulin 2024, wanda ma’ikatar kudi ta fitar.

Ma’ikatar kudin, ta yi bayani kan dakatar da shirin bayar da damar shigo da kayan abinci cikin kasar da suka hada da; Shinkafa, Alkama, Masara da kuma wasu sauran kayan abincin.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Har ila yau, gwamnatin ta yi yunkurin bayar da damar shigo da kayan abincin ne, domin saukaka tsadar kayan abincin a Nijeriya.

Kudin fiton kayan abincin da suka hada da Shinkafa, Dawa da kuma Wake, ya kai daga kashi 5 zuwa kashi 30.

An Dora Alhakin Rashin Bayar Da Damar Shigo Da Kayan Abincin Kan Ma’aikatar Kudi:

Mai magana da yawun Hukumar Hana Fasakwuri ta Kasa, Abdullahi Maiwada; a makon da ya gabata, ya dora alhakin rashin bayar da damar shigo da kayan abincin a kan ma’aikatar kudi.

Maiwada, a hirarsa da jaridar BusinessDay a watan Satumbar 2024, ya dora laifin a kan ma’aikatar kudin; kan jinkirin wanzar da damar barin shigo da kayan abincin cikin kasar.

A cewarsa, ma’aikatar ta gaza mika jerin sunayen masu shigo da kayan da kuma sauran kamfanonin da suka cika sharuddan shigo da kayan abincin kamar yadda aka tsara.

“Kamar yadda Hukumar Kwastan ta Kasa, ta isar da tsare-tsaren shigo da kayan abincin; da ma’aikatar kudin ta amincewa tar da bayar da dama, da tuni an fara wanzar da shirin bayar da umarnin shigo da kayan”, in ji Maiwada.

Ya ci gaba da cewa, “Amma tun bayan da tsarin barin shigo da kayan ya fito daga ma’aikatar kudin, ya kamata a ce ta bayar da jerin sunayen wadanda suka cancanta su shigo da kayan”.

Wani bincike da jaridar ta BusinessDay ta gudanar ya nuna cewa, har zuwa watan Disambar 2024, ma’aikatar kudin ba ta tura wa Hukumar Kwastan jerin sunayen masu shigo da kayan ba; sannan kuma ba ta yi wani gamsasshen bayani ba.

Ci Gaba Da Fuskantar Barazanar Yunwa A Kasar:

Fiye da mutum 67 ne, ciki har da kanannan yara suka rasa rayukansu a turmutsutsun rabon kayan abinci a Nijeriya, daidai lokacin shagulgulan bikin karshen shekarar 2024; a wasu sassan kasar.

Wasu masu fashin baki kan al’amuran yau da kullum sun bayyana cewa, lamarin ya nuna a zahiri irin matsananciyar yunwar da talakawan kasar ke ci gaba da fuskanta.

Shirin samar da abinci na Majalisar Dinkin Duniya (WFP) a farkon shekarar 2024 ya bayyana cewa, ‘yan Nijeriya miliyan 33 ne za su fuskanci yunwa a 2025, ban da kuma wasu daga cikin ‘yan kasar kimanin miliyan 25 da suka fuskanci yunwar a 2024.

Mai magana da yawun shirin na WFP, Chi Lael; ya sheda wa manema labarai a taron Geneba na 2024 cewa, ‘yan Nijeriya da dama; abincin da za su ci ya gagare su.

Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu, ta kirkiro da tsauraran matakai na bunkasa tattalin arzikin kasar, ciki har da cire tallafin mai da sauran makamantansu cikin daukacin fadin kasar.

A watan Nuwambar da ya gabata, an samu hauhawar farashin kayayyaki da kashi 34.6, da ya haura wanda aka taba samu cikin shekaru 28 a kasar, inda farashin kayan abinci ya karu da kashi 39.9 a shekarar 2024.

Wani rahoton girke-girke da aka fitar ya nuna cewa, a watan Satumbar 2024, magidanci mai ‘ya’ya biyar, na kashe akalla 21,300 cikin wata hudu idan zai dafa hadaddiyar Shinkafa, inda hakan ya karu da kashi 5.1 cikin 100.

A yanzu haka, ana sayar da buhun Shinkafa mai nauyin kilo 50; wacce ake shigo da ita daga waje da kuma wadda ake nomawa a kasar, kan Naira 100,000, inda farashinsu ya dara sabon mafi karancin albashin ma’aikata na Naira 70,000.

Bugu da kari, farashin kayan abinci da suka hada da Wake, Rogo, Dankali da sauransu, sun yi tashin gwauron zabi da kashi 100 cikin shekara daya tare kuma da kalubalen rashin tsaro da ya kara haddasa hakan.

Wani mai suna Daniel Brown, a fannin shigo da kaya cikin kasar ya bayyana cewa, “Tsadar kayan abinci ta karu a kasar, sakamakon rashin aiwatar da tsarin da gwamnatin ta gaza yi a watan Julin  2024”.

“Sai dai, rashin wanzar da wannan tsari; ya nuna a zahiri gazawar hukumomin gwamnatin taraya, wanda hakan ya kara jefa rayuwar talakawan kasar cikin wata matsalar daban”, in ji Brown.

Yunwa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Dalilin Rahoton Farfesa Jega Na Bukatar Taimaka Wa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona

Dalilin Rahoton Farfesa Jega Na Bukatar Taimaka Wa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona

LABARAI MASU NASABA

Yunwa

Sojoji Sun Ceto Mutane 13 Da ’Yan Bindiga Suka Yi Garkuwa Da Su

September 11, 2026
Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

September 11, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

September 11, 2026
Yunwa

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026
Yunwa

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

September 11, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2026 Kwamared Nasir Idris

September 11, 2026
Yunwa

Dalilin Da Ya Sa Ba Zan Janye Wa Atiku Ba A Zaɓen 2027 – Peter Obi

September 11, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

Gwarzon Shekarar 2026 Abdulsamad Rabiu

September 11, 2026
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Buƙatar Ɗaukar Matakan Daƙile Yaɗuwar Cutar Mashaƙo A Nijeriya

September 11, 2026
Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.