Fitaccen Fasto a Jihar Kaduna, Dakta Yohanna Buru, ya karrama malamin addinin Musulunci, Sheikh Usman Mohammed Mai-Mota Gwalli, da lambar yabo ta musaman, kan yadda ya shafe sama da 50, yana koyar da karatun alƙur’ani mai tsarki, hadisai da tafsir da kuma harshen Larabci ga yara da matasa Musulmai da ke a sassa daban-daban na arewacin Nijeriya.
Buru ya miƙa masa lambar yabon ce a makarantar malamin da ke a yankin Ɗan Mani a gudundumar Rigasa a Kaduna, yayin da ya jagoranci tawagawar wasu fastoci.
Ya ce ya karrama Sheikh Usman ne domin ƙara ƙarfafa masa guiw, kan ci gaba da ilimantar da yara da matasa, musamman duk da tsufan da malamin yake da shi.
Buru ya ce, bisa wasu bayanai da ya samu kan malamin, sun nuna cewa a tarihin koyarwarsa, ya ilimantar da sama da matasa 10,000 a fannoni daban-daban na ilimin addinin Musulunci, inda wasu daga cikinsu sun zama malamai.
Ya ce, batun ba wai na karramawa ne kawai ba, amma domin a ƙara ƙarfafa fahimtar zumunci a tsakanin mabiya addinin Kirista da kuma Musulmai.
Shi ma, a nasa jawabin, Fasto Emmanuel John, ya danganta gundunmawar da Sheikh Usman ke ci gaba da bayarwa a matsayin wadda al’ummar Musulmai ba za su iya mantawa da ita ba.
Sheikh Usman ya bayyana karramar a matsayin ita ce ta farko da ya taɓa samu bayan shafe sama da shekaru 50 yana koyarwa, inda kuma ya gode wa Buru kan wannan karramawar.














