a zuba jari irin na ƙasar nan, domin ƙara haɓaka nomanta da kuma samun riba.
Sanawar ta ƙara da cewa, shugaba Tinubu ya kuma amince da a riƙa yin amfani da tsarin da hukumar NCƊ ta ƙirƙiro, wajen fitar da kaya da kuma cire duk wani takunkumi na barin ana fitar da Kaɗanyar daga cikin ƙasar nan zuwa ƙasashen ƙetare.
Haka zalika, shugaban ƙasar ya kuma bayar da umarnin cewa; duk wata Kaɗanyar da ta yi saura, a riƙa fitar da ita ta hanyar amfani da hukumar ta NCƊ kaɗai, bisa ƙa’idojin d aka gindaya.
- Harin Ƴan Bindiga A Zamfara: Gwamna Lawal Ya Jagoranci Taron Gaggawa Kan Tsaro
- Mahangar Wakiliya Mai Fasahar Wasan Kwaikwayo Game Da Dimokuradiyyar Dake Shafar Kowa Da Kowa A Nan Kasar Sin
Kazalika, shugaba Tinubu ya kuma umarci ma’aikatar kuɗi ta tarayya da ta samar da damar samar da kuɗi a ƙarƙashin shirin tallafi na NESS, musamman domin hakan ya bai wa ma’aikatar masana’antu, kasuwanci da zuba jari, damar ƙaddamar da samar da kuɗaɗe, domin ƙarfafa rayuwar manoman da ke noman Kaɗanyar a ƙasar.
Ana dai amfani da manta ne, wajen sarrafa shi zuwa nau’ikan man shafawa na jiki da kuma gyaran gashi tare da sarrafa man zuwa man girki.
Tuni dai, gwamnatin tarayya ta ci gba da ƙarfafa ƙwarin guiwar saffara ta a cikin ƙasar.
“Gwamnatin tarayya, ta himmatu wajen samar da tsare-tsaren ƙara ɗaga darajar nomanta, musamman ganin cewa; fanni ne da ake ci gaba da gudanar da gasarsa a fagen aikin noma a dukkanin faɗin duniya,“ in ji sanawar.
Gwamnatin ta ƙara tsawaita wa’adin haramcin fitar da Kaɗanyar ne, biyo bayan ƙarewar wa’adi na wata shida, na haramta fitar da ita, da ta bayar da umarni a watan Agustan shekarar 2025.















Discussion about this post