ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Tabka Asarar Manoma A Noman Tattasan Rani Na Bana

by Abubakar Abba
2 months ago

Wasu daga cikin manoma da suka yi noman rani na tattasai, musamman nau’in da ake kira a turance ‘scotch bonnet habanero’, a Arewacin kasar nan, sun tabka mummunar asara mai yawa.

Kazakila, su ma wasu diloli na tattasan da suka saro shi daga wasu kasuwannin da ke yankin, asarar ta shafe su kai tsaye.

Hakan ya faru ne dai, biyan faduwar farashin tattasan, inda hakan ke ci gaba da jefa su cikin damuwa sakamakon asarar da suka tafka.

ADVERTISEMENT

Daya daga cikin manoman nau’ikan tattasan, Alhaji Muhammed Sani Sulaiman, wanda yake zaune a Karamar Hukumar Saminaka ta Jihar Kaduna, ya sanar da cewa; mafi akasarin manoman, ba su samu wata riba ta a zo a gani ba, bayan sun kammala girbi.

Ya kara da cewa, ya kashe dimbin kudaden da suka kai kusan kimanin naira miliyan bakwai wajen  sayen takin zamani da man fetur, wanda ya zuba a injin ban ruwa domin yin noma da kuma takin gargajiya da sayen maganin kashe kwari, amma kuma farashin amfanin ya sai ya yi matukar raguwa.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

Ya ci gaba da cewa, a baya kafin faduwar farashinsu, suna sayar da duk buhu daya na nau’ikan biyu a kan sama da naira 30,000, inda ya kara da cewa; amma a noman ranin da suka yi na bana, ko naira 200,000, manoman ba su iya samu ba bayan sun yi girbi.

Shi ma wani manomin mai suna Haruna Idris, ya bayyana cewa; a farko, duk buhu daya na nau’ikan biyu, ana sayarwa ne a kan naira 30,000, amma daga baya, farashin ya sauka zuwa naira 4,000.

Ya ce, ya san cewa; akwai wasu manoman da suka sayar da gonakinsu da gidajensu da sauran makamantansu, domin zuba jari a noman nau’ikan tattasan biyu, amma bayan faduwar farashinsu, sai suka tabka mummunar asara.

Kazalika, shi ma wani manomin mai suna Ibrahim Abubakar Aminu, wanda kuma shi ne, shugaban ‘yan kasuwa masu sayar da tumatir a kasar, wanda yake  zaune Karamar Hukumar Saminaka ya sanar da cewa; manoman sun fuskanci matsaloli daban-daban a kakar noman ranin ta bana.

A cewarsa, a shekarar da ta wuce, an sayar da duk buhu daya na nau’ikan a kan naira 50,000 zuwa naira 55,000, amma a kakar noman bana, farashin nau’ikan biyu, ya ragu daga naira  5,000 zuwa naira 7,000, inda hakan ya sanya manoman yin asara mai dimbin yawa.

Shi kuwa wani dan kasuwa mai suna Sani Zubairu Garko, a yankin na Saminaka cewa ya yi, su ma ba su samu wata ribar kirki wajen sayar da amfanin biyu ba.

Haka nan, shi ma wani mai suna Malam Ibrahim Zakariya Dan Kaduna, wanda dilan sayar da tumatir ne a yankin Saminaka, ya sanar da cewa; manoman sun fara fuskantar wannan matsala ce, tun kafin bikin Kirisimeti na bana.

“Mun kai buhunhunan tattasan zuwa kasuwannin da ke Jihar Legas, inda muka sayar da duk buhu guda a kan naira 1,000,“ in ji shi.

“Har yanzu, akwai wasunmu da ake bi bashi, domin mun ciwo bashi ne, don mu kara habaka hada-hadar kasuwancinmu, amma kuma sai muka tafka wannan asara,” a cewar tasa.

Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

MASU ALAKA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
Noma Da Kiwo

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

June 12, 2026
Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
Noma Da Kiwo

Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

June 6, 2026
Next Post
Sin Da Somalia Sun Kaddamar Da Cibiyar Bincike Game Da Salon Zamanantarwa Irin Na Sin

Sin Da Somalia Sun Kaddamar Da Cibiyar Bincike Game Da Salon Zamanantarwa Irin Na Sin

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tunisiyya Ta Sallami Kocinta Bayan Shan Kashi 5-1 A Wasan Farko Na Kofin Duniya

Tunisiyya Ta Sallami Kocinta Bayan Shan Kashi 5-1 A Wasan Farko Na Kofin Duniya

June 15, 2026
Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

June 15, 2026
ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

June 15, 2026
Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

June 15, 2026
Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

June 15, 2026
Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

June 15, 2026
An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.