Wasu daga cikin manoma da suka yi noman rani na tattasai, musamman nau’in da ake kira a turance ‘scotch bonnet habanero’, a Arewacin kasar nan, sun tabka mummunar asara mai yawa.
Kazakila, su ma wasu diloli na tattasan da suka saro shi daga wasu kasuwannin da ke yankin, asarar ta shafe su kai tsaye.
Hakan ya faru ne dai, biyan faduwar farashin tattasan, inda hakan ke ci gaba da jefa su cikin damuwa sakamakon asarar da suka tafka.
Daya daga cikin manoman nau’ikan tattasan, Alhaji Muhammed Sani Sulaiman, wanda yake zaune a Karamar Hukumar Saminaka ta Jihar Kaduna, ya sanar da cewa; mafi akasarin manoman, ba su samu wata riba ta a zo a gani ba, bayan sun kammala girbi.
Ya kara da cewa, ya kashe dimbin kudaden da suka kai kusan kimanin naira miliyan bakwai wajen sayen takin zamani da man fetur, wanda ya zuba a injin ban ruwa domin yin noma da kuma takin gargajiya da sayen maganin kashe kwari, amma kuma farashin amfanin ya sai ya yi matukar raguwa.
Ya ci gaba da cewa, a baya kafin faduwar farashinsu, suna sayar da duk buhu daya na nau’ikan biyu a kan sama da naira 30,000, inda ya kara da cewa; amma a noman ranin da suka yi na bana, ko naira 200,000, manoman ba su iya samu ba bayan sun yi girbi.
Shi ma wani manomin mai suna Haruna Idris, ya bayyana cewa; a farko, duk buhu daya na nau’ikan biyu, ana sayarwa ne a kan naira 30,000, amma daga baya, farashin ya sauka zuwa naira 4,000.
Ya ce, ya san cewa; akwai wasu manoman da suka sayar da gonakinsu da gidajensu da sauran makamantansu, domin zuba jari a noman nau’ikan tattasan biyu, amma bayan faduwar farashinsu, sai suka tabka mummunar asara.
Kazalika, shi ma wani manomin mai suna Ibrahim Abubakar Aminu, wanda kuma shi ne, shugaban ‘yan kasuwa masu sayar da tumatir a kasar, wanda yake zaune Karamar Hukumar Saminaka ya sanar da cewa; manoman sun fuskanci matsaloli daban-daban a kakar noman ranin ta bana.
A cewarsa, a shekarar da ta wuce, an sayar da duk buhu daya na nau’ikan a kan naira 50,000 zuwa naira 55,000, amma a kakar noman bana, farashin nau’ikan biyu, ya ragu daga naira 5,000 zuwa naira 7,000, inda hakan ya sanya manoman yin asara mai dimbin yawa.
Shi kuwa wani dan kasuwa mai suna Sani Zubairu Garko, a yankin na Saminaka cewa ya yi, su ma ba su samu wata ribar kirki wajen sayar da amfanin biyu ba.
Haka nan, shi ma wani mai suna Malam Ibrahim Zakariya Dan Kaduna, wanda dilan sayar da tumatir ne a yankin Saminaka, ya sanar da cewa; manoman sun fara fuskantar wannan matsala ce, tun kafin bikin Kirisimeti na bana.
“Mun kai buhunhunan tattasan zuwa kasuwannin da ke Jihar Legas, inda muka sayar da duk buhu guda a kan naira 1,000,“ in ji shi.
“Har yanzu, akwai wasunmu da ake bi bashi, domin mun ciwo bashi ne, don mu kara habaka hada-hadar kasuwancinmu, amma kuma sai muka tafka wannan asara,” a cewar tasa.















Discussion about this post