ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Tabka Asarar Manoma A Noman Tattasan Rani Na Bana

by Abubakar Abba
2 months ago

Wasu daga cikin manoma da suka yi noman rani na tattasai, musamman nau’in da ake kira a turance ‘scotch bonnet habanero’, a Arewacin kasar nan, sun tabka mummunar asara mai yawa.

Kazakila, su ma wasu diloli na tattasan da suka saro shi daga wasu kasuwannin da ke yankin, asarar ta shafe su kai tsaye.

Hakan ya faru ne dai, biyan faduwar farashin tattasan, inda hakan ke ci gaba da jefa su cikin damuwa sakamakon asarar da suka tafka.

ADVERTISEMENT

Daya daga cikin manoman nau’ikan tattasan, Alhaji Muhammed Sani Sulaiman, wanda yake zaune a Karamar Hukumar Saminaka ta Jihar Kaduna, ya sanar da cewa; mafi akasarin manoman, ba su samu wata riba ta a zo a gani ba, bayan sun kammala girbi.

Ya kara da cewa, ya kashe dimbin kudaden da suka kai kusan kimanin naira miliyan bakwai wajen  sayen takin zamani da man fetur, wanda ya zuba a injin ban ruwa domin yin noma da kuma takin gargajiya da sayen maganin kashe kwari, amma kuma farashin amfanin ya sai ya yi matukar raguwa.

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

Ya ci gaba da cewa, a baya kafin faduwar farashinsu, suna sayar da duk buhu daya na nau’ikan biyu a kan sama da naira 30,000, inda ya kara da cewa; amma a noman ranin da suka yi na bana, ko naira 200,000, manoman ba su iya samu ba bayan sun yi girbi.

Shi ma wani manomin mai suna Haruna Idris, ya bayyana cewa; a farko, duk buhu daya na nau’ikan biyu, ana sayarwa ne a kan naira 30,000, amma daga baya, farashin ya sauka zuwa naira 4,000.

Ya ce, ya san cewa; akwai wasu manoman da suka sayar da gonakinsu da gidajensu da sauran makamantansu, domin zuba jari a noman nau’ikan tattasan biyu, amma bayan faduwar farashinsu, sai suka tabka mummunar asara.

Kazalika, shi ma wani manomin mai suna Ibrahim Abubakar Aminu, wanda kuma shi ne, shugaban ‘yan kasuwa masu sayar da tumatir a kasar, wanda yake  zaune Karamar Hukumar Saminaka ya sanar da cewa; manoman sun fuskanci matsaloli daban-daban a kakar noman ranin ta bana.

A cewarsa, a shekarar da ta wuce, an sayar da duk buhu daya na nau’ikan a kan naira 50,000 zuwa naira 55,000, amma a kakar noman bana, farashin nau’ikan biyu, ya ragu daga naira  5,000 zuwa naira 7,000, inda hakan ya sanya manoman yin asara mai dimbin yawa.

Shi kuwa wani dan kasuwa mai suna Sani Zubairu Garko, a yankin na Saminaka cewa ya yi, su ma ba su samu wata ribar kirki wajen sayar da amfanin biyu ba.

Haka nan, shi ma wani mai suna Malam Ibrahim Zakariya Dan Kaduna, wanda dilan sayar da tumatir ne a yankin Saminaka, ya sanar da cewa; manoman sun fara fuskantar wannan matsala ce, tun kafin bikin Kirisimeti na bana.

“Mun kai buhunhunan tattasan zuwa kasuwannin da ke Jihar Legas, inda muka sayar da duk buhu guda a kan naira 1,000,“ in ji shi.

“Har yanzu, akwai wasunmu da ake bi bashi, domin mun ciwo bashi ne, don mu kara habaka hada-hadar kasuwancinmu, amma kuma sai muka tafka wannan asara,” a cewar tasa.

Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Matatar Ɗangote Ta Ƙaryata Iƙirarin Dillalan Man Fetur 

MASU ALAKA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 
Noma Da Kiwo

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
Next Post
Sin Da Somalia Sun Kaddamar Da Cibiyar Bincike Game Da Salon Zamanantarwa Irin Na Sin

Sin Da Somalia Sun Kaddamar Da Cibiyar Bincike Game Da Salon Zamanantarwa Irin Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

July 8, 2026
Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

July 8, 2026
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

July 8, 2026
Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.