ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

by Idris Aliyu Daudawa
9 months ago
Hutu

A garin Nyanya, da yake ƙarƙashin Babban Birnin Tarayya Abuja, matar aure, Hauwa Moji, ita ma ta bada labarin irin yadda suke fuskantar lamarin. Ta bayyana cewa ‘ya’yanta b za su ci gaba da karatu ba a wannan zangon ba, domin komai ba sai saboda an ƙara kuɗin haya da kuma na makaranta, tace irin wannan lamarin da zai laƙume kuɗaɗe masu yawa mijinta ba zai iya ɗaukar nauyin abubuwan ba a lokaci ɗaya.

Ta ce, “Matsalar ta fara ne bayan da minjinta ya rasa aikin koyarwa da yake yi ya fara neman wani. Cikin ikon Allah sai ya samu wani amma kafin a daga hutu. Wani abin takaici dole ne ya fita daga gidan da aka ba shi makarantar da ya ajiye aiki, hakan ya nuna dole ne ya nemi wani wurin zama.

“Ta ci gaba da bayanin mijina daga ƙarshe ya samu wuri a Nyanya. Maigidan yace zai biya Naira 400, 000, amma saboda baya kusa, sai mai bada hayar ya ce, bayan ya amshi wasu ƙarin kuɗi, sai ya tsaya kai da fata cewa dole ne sai ya biya Naira 700, 000 a shekara ta farko saboda akwai kuɗin da ake ba mai bada haya, kuɗin Lauya, da kuma sauran wasu kuɗaɗe daban, daga nan kuma shekara mai zuwa sai ya biya, Naira 400,000 .

ADVERTISEMENT
  • Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta
  • ‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

“Bai da zaɓi dole ya haɗa ya biya da kuɗaɗen da yara ya kamata a biya ma su kuɗin makaranta, maimakon haka sai ya biya kuɗinhaya suka shiga cikin gidan. Ta ci gaba da ƙarin bayani.Bamu da abinda ya dace mu yi wanda fi wanda muka yi, amma ba maganar fara karatun yara ba a wannan zangon, sai kuma lokacin da abubuwa suka fara gyaruwa su ci gaba da karatu.

Ita kuma Gloria Oche, da take da ‘ya’ya uku ya bayyanawa LEADERSHIP cewa ‘yar’uwarta tana tunanin ko za ta ɗauki mataki da ta san zai fishshe ta.

LABARAI MASU NASABA

Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa

An Daƙile Yunƙurin Sace Ɗalibai Masu Zana Jarabawar WASSCE A Kogi

Kamar yadda Oche, wadda ‘ya’yan ‘yar’uwarta suke zuwa makarantar Reno ta Oluwami da Firmare , da take Abuja inda shekarun baya suke biyan wajen Naira 600,000 ko wane zangon karatu, saboda wasu haraje- harajen da aka haɗa da su ciki.

“Maganar gaskiya kowace shekara idan za’a shiga sabon zangon karatu, makarantu su kan ƙara kuɗin makaranta, su ƙara wasu sabbin abubuwa, kamar su kuɗin ICT, wasanni tsaro. Sai dai ƙarin da akwai matuƙar matsala.”

A makarantar( Prime School ) da ke, Karu,inda aka ƙiyasta ana biyan kusan Naira 300, 000, kowane zangon karatu,wani Malamin da baya son a ambaci sunansa ya ce, akwai ƙarin kuɗin makaranta waɗanda suna da alaƙa ne da lamarin daya shafi kayn zuwa makaranta, bunƙasar makaranta, da kuma sauran abubuwa.

“Idan aka dukkan ƙarurrukan da aka yi abin zai zama da akwai ɗaure kai. Kuɗin haya ya ƙaru a wannan unguwa idan kuma mutum ya yi bincike kuma za a gane irin mutanen da suke zama a wurin, waɗanda abinda suke samu ba kasafai yake biya masu buƙata ba. Don haka idan har ka sa ɗanka wannan makaranta,duk da yake dai z aka, iya biya,amma idan wani babban abu ya taso kamar kiuɗin haya abin sai dai ayi shiru kamar yadda ya ce,”.

Wani mahaifi, Joseph Hange wanda ‘yarsa take zuwa makarantar Bright Child Academy, Lugbe, cewa ya yi sabuwar shekarar karatun ta zo da abubuwa masu sosai zuciya.

“Abin bai tsaya kan maganar ƙare-ƙaren kuɗaɗen bane kawai na kuɗin makaranta, abinci, Littattafai, suturar zuwa makaranta, ziyarar buɗe ido, duk a haɗa su wuri ɗaya. Kamar su da suke harkar kasuwanci, lamarin tattalin arzikin ba shi da daɗi.Cewa ya yi sun tattauna a gida ko daga ƙarshe irin wannan tafiyar za ta ɗore”.

Yayin da Iyaye lamarin ya hana su kwanciyar hankali,su ma Malaman makarantar kamar duk jirgi ɗaya ya ɗauko su.Domin kuwa yawancin makarantu yawan ƙarin kuɗin makaranta bai kai wag a ƙarin albashi ga su Malaman makarantar.

Wani Malami mai suna Moses Sachi a Abuja shi ma abin ya dame shi, saboda kuwa cewa yayi “Muna dai jin Iyaye suna kokawa, amma mu ma a matsayinmu na Malamai, matsalar da take damun Iyayen yaran muma ita ce ke damun mu .Lamarin kuɗin haya, abinci, da zirga- zirga abin yana ci mana tuwo a ƙwarya.

Wasu daga cikinmu akwai ayyukan da muke yi domin a samu tsira da mutunci kamar, zuwa koyar da darussa a gida, ƙananan sana’oi, kawai saboda dai mu samu kulawa da Iyali . Wasu makarantu sun ɗan yi ƙarin albashi wanda bai maganin matsin tattalin arzikin da kowa yake fuskanta ba, bama kamar talaka kamar yadda ya jaddada” .

Binciken da LEADERSHIP ta yi rahoton ya nuna matslar ba kawai ta ƙare bane kan ƙarin kuɗin makaranta ba.Kuɗaɗen haya sun ƙaru a sassa daban daban kamar su Abuja, Legas, da kuma wasu manyan wurare kamar Karu, Lugbe, da Gwarimpa da sauarn sassan Babban Birnin Tarayya Abuja, masu gidaje sun ƙara kuɗin haya da kashi 30 kamar yadda binciken ya nuna

Shi yasa Iyayen da suke biyan kuɗin makaranta dubban Nairori yanzu dole ne su san irin hanyar da za su bi, domin su nemi ƙarin kuɗin da za su cika domin biyan haya.

Wani mahaifi a Nyanya, mai suna Isaac Terseer, ya yi lamarin kallon abinda zai yi wuyar jurewa:

Inda ya ce “Wannan tamkar mutum ya riƙa bin inuwa ne da ƙoƙarin kamata.An ƙara kuɗin makaranta, kuɗin haya sun ƙaru.

Wannan halin ƙuncin rayuwa tana sa mutane ko iyalai su cikin halin ni’yasu kan yadda za su yanke shawarar daga cikin abubuwan da suka kamata su yi su ɗauki ɗaya da suke ma kallpon ya fi muhimmanci. Wasu na canza wa ‘ya’yansu makaranta zuwa wadda kuɗin da za su iya biya.Wasu suna tunanin yanke shawarar a riƙa koya masu a gida, ko kuma maida su makarantun gwamnati duk kuwa da yake akwai matsalar kayan aiki da, da rashin nagartar koyarwar.

An samu bayanan da suke nuna Iyaye na biyan tsakanin Naira milyan 3 zuwa 5 kowane zangon karatu.

Ta ɓangaren tsaka- tsaki ana biyan Naiar 800,000 zuwa milyan 2.5 kowane zangon karatu.

Waɗanda ake ma kallon masu sassauci ne a Abuja ana biyan Naira 120,000 zuwa 200, 000 a kowane zangon karatu.

Hutu
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

MASU ALAKA

Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa
Manyan Labarai

Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa

June 10, 2026
Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci
Manyan Labarai

An Daƙile Yunƙurin Sace Ɗalibai Masu Zana Jarabawar WASSCE A Kogi

June 10, 2026
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
Manyan Labarai

Babu Makarantar Da Aka Kai Wa Hari A Neja – ‘Yansanda

June 10, 2026
Next Post
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

'Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

An Kafa Yanki Mafi Girma Na Hade Ayyukan Samar Da Wutar Lantarki Da Sarrafa Makamashin Hydrogen Da Adana Makamashi A Kasar Sin

An Kafa Yanki Mafi Girma Na Hade Ayyukan Samar Da Wutar Lantarki Da Sarrafa Makamashin Hydrogen Da Adana Makamashi A Kasar Sin

June 10, 2026
Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa

Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa

June 10, 2026
An Kaddamar Da Taron Dandalin Tattauna Hadin Gwiwar Fasahohi Da Masana’antun Aikin Gona na Sin Da Afirka A Kenya

An Kaddamar Da Taron Dandalin Tattauna Hadin Gwiwar Fasahohi Da Masana’antun Aikin Gona na Sin Da Afirka A Kenya

June 10, 2026
NNPCL

Zargin Sace Naira Tiriliyan 210: Majalisa Ta Bayar da Umarnin Kama Tsohon Shugaban NNPC, Mele Kyari

June 10, 2026
Wakilin Sin: Bangaren Sin Yana Goyon Bayan Kasashen Afirka a Fannin Magance Matsalolin Nahiyar Bisa Hanyoyin Da Suka Dace Da Su

Wakilin Sin: Bangaren Sin Yana Goyon Bayan Kasashen Afirka a Fannin Magance Matsalolin Nahiyar Bisa Hanyoyin Da Suka Dace Da Su

June 10, 2026
An Kashe ’Yan Bindiga Biyu A Abuja

An Kashe ’Yan Bindiga Biyu A Abuja

June 10, 2026
Ko Me Ya Sa Alkaluman Rahotan Cinikayyar Waje Na Sin Suka Nuna Karuwar Nasarori Fiye Da Yadda Aka Yi Tsammani?

Ko Me Ya Sa Alkaluman Rahotan Cinikayyar Waje Na Sin Suka Nuna Karuwar Nasarori Fiye Da Yadda Aka Yi Tsammani?

June 10, 2026
Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi

Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi

June 10, 2026
An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026

An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026

June 10, 2026
Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje

Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje

June 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.