ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

by Idris Aliyu Daudawa
4 days ago

A duk yayin da mace ta ɗauki ciki, tana samun kanta a wani irin yanayi maras daɗi har sai ta haihu, don haka; batun juna biyu ba ƙaramin al’amari ba ne, sakamakon zuwa da ya ke yi da haɗari iri daban-daban.

Wasu matan, bayan sun ɗauki ciki ne suke haɗuwa da cututtuka da dama; kamar ciwon zuciya, ciwon siga, hawan jini da sauran makamantansu. Don haka, a nan ya kamata a sani cewa; babu yadda za a yi mace ta ɗauki ciki ba tare da jikinta ya canza ba.

Wannan dalili ne ya sa, idan nauyin mai juna biyu bai kai yadda ake buƙata ba, sai a ja hankalinta ta yi wasu abubuwa da za su sa nauyin nata ya ƙaru, haka nan; idan nauyin nata ya yi yawa, musamman ga mata masu ƙiba; nan ma a kan ja hankalinsu su yi ƙoƙari wajen rage nauyin nasu.

ADVERTISEMENT

Saboda haka, da zarar an ce mace na da ciki; abubuwa da dama na sauya yanayin jikinta, wata ta ƙara ƙiba, wata ƙuraje su feso mata a fuska, wata kalar fatarta ta canja; wani wajen ya yi fari wani ya yi baƙi, wasu su yi ta samun ƙananan cututtuka, wasu amai, wasu kuma saboda damuwa su yi ta faman kuka ba tare da an yi musu komai ba.

Don haka, ya zama wajibi maza su riƙa yi wa matansu uzuri a yayin da suke ɗauke da juna biyu da kuma bayan sun haihu. Misali, babu yadda za a yi a ce mace ta ɗauki ciki tsawon wata tara tana tare da shi, sannan bayan ta haihu a kuma yi tunanin cewa; wannan ciki nata zai dawo kamar yadda yake a baya.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

Har ila yau, maza da dama na da irin wannan ɗabi’a ta tsangwamar matansu, sakamakon yadda jikinsu yake sauyawa bayan sun haihu, musamman ganin yadda cikinsu yake yin shaida ko tattarewa ko kuma girma ta hanyar samun tumbi.

Irin wannan tsangwamar da maza ke yi wa mata, ko kaɗan bai dace ba; domin kuwa wasu matan na shiga cikin mummunan hali tare da takurawa kansu, ta hanyar kashe kuɗaɗensu don ganin sun samu maganin wannan matsala, wadda babu yadda za a yi a iya magance ta, tunda halittar ce a haka; kamar shekaru ne duk yadda za ka yi, babu wata dabara da za ta iya ɓoye su.

Saboda haka, mata ya kamata ku kiyaye; ku daina zuwa kuna kashe kuɗaɗenku babu gaira babu dalili, amma babu wani magani da za a baki ki sha tumbinki ya tafi, wasu sai su sha magani su je su yi ta zawo haka kawai, wai don tunbinsu ya ragu.

A nan, muna ƙara jan hankalin maza; su ji tsoron Allah su riƙa tausaya wa matayensu, musamman bayan sun samu juna biyu sun haihu. Sannan ku tuna cewa, wannan ciki da yake canja wa mata wasu ɓangarori na jikinsu, ku ne kuke yi musu ba daga gidajensu suke zuwa da shi ba.

Daga rumbun Dakta Na’ima Abubakar

Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Ƙaruwar Kuɗaɗen Shiga Ga Jihohin Nijeriya Talauci Na Ƙaruwa

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Ilimi

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa (Hedimasta) (1)

May 23, 2026
Next Post
Sin Ta Kalubalanci Kwamitin Sulhun MDD Da Ya Gyara Ko Soke Takunkumin Da Aka Kakabawa Sudan Ta Kudu

Sin Ta Kalubalanci Kwamitin Sulhun MDD Da Ya Gyara Ko Soke Takunkumin Da Aka Kakabawa Sudan Ta Kudu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.