A duk yayin da mace ta ɗauki ciki, tana samun kanta a wani irin yanayi maras daɗi har sai ta haihu, don haka; batun juna biyu ba ƙaramin al’amari ba ne, sakamakon zuwa da ya ke yi da haɗari iri daban-daban.
Wasu matan, bayan sun ɗauki ciki ne suke haɗuwa da cututtuka da dama; kamar ciwon zuciya, ciwon siga, hawan jini da sauran makamantansu. Don haka, a nan ya kamata a sani cewa; babu yadda za a yi mace ta ɗauki ciki ba tare da jikinta ya canza ba.
Wannan dalili ne ya sa, idan nauyin mai juna biyu bai kai yadda ake buƙata ba, sai a ja hankalinta ta yi wasu abubuwa da za su sa nauyin nata ya ƙaru, haka nan; idan nauyin nata ya yi yawa, musamman ga mata masu ƙiba; nan ma a kan ja hankalinsu su yi ƙoƙari wajen rage nauyin nasu.
Saboda haka, da zarar an ce mace na da ciki; abubuwa da dama na sauya yanayin jikinta, wata ta ƙara ƙiba, wata ƙuraje su feso mata a fuska, wata kalar fatarta ta canja; wani wajen ya yi fari wani ya yi baƙi, wasu su yi ta samun ƙananan cututtuka, wasu amai, wasu kuma saboda damuwa su yi ta faman kuka ba tare da an yi musu komai ba.
Don haka, ya zama wajibi maza su riƙa yi wa matansu uzuri a yayin da suke ɗauke da juna biyu da kuma bayan sun haihu. Misali, babu yadda za a yi a ce mace ta ɗauki ciki tsawon wata tara tana tare da shi, sannan bayan ta haihu a kuma yi tunanin cewa; wannan ciki nata zai dawo kamar yadda yake a baya.
Har ila yau, maza da dama na da irin wannan ɗabi’a ta tsangwamar matansu, sakamakon yadda jikinsu yake sauyawa bayan sun haihu, musamman ganin yadda cikinsu yake yin shaida ko tattarewa ko kuma girma ta hanyar samun tumbi.
Irin wannan tsangwamar da maza ke yi wa mata, ko kaɗan bai dace ba; domin kuwa wasu matan na shiga cikin mummunan hali tare da takurawa kansu, ta hanyar kashe kuɗaɗensu don ganin sun samu maganin wannan matsala, wadda babu yadda za a yi a iya magance ta, tunda halittar ce a haka; kamar shekaru ne duk yadda za ka yi, babu wata dabara da za ta iya ɓoye su.
Saboda haka, mata ya kamata ku kiyaye; ku daina zuwa kuna kashe kuɗaɗenku babu gaira babu dalili, amma babu wani magani da za a baki ki sha tumbinki ya tafi, wasu sai su sha magani su je su yi ta zawo haka kawai, wai don tunbinsu ya ragu.
A nan, muna ƙara jan hankalin maza; su ji tsoron Allah su riƙa tausaya wa matayensu, musamman bayan sun samu juna biyu sun haihu. Sannan ku tuna cewa, wannan ciki da yake canja wa mata wasu ɓangarori na jikinsu, ku ne kuke yi musu ba daga gidajensu suke zuwa da shi ba.
Daga rumbun Dakta Na’ima Abubakar















Discussion about this post