ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

by Idris Aliyu Daudawa
4 weeks ago

A duk yayin da mace ta ɗauki ciki, tana samun kanta a wani irin yanayi maras daɗi har sai ta haihu, don haka; batun juna biyu ba ƙaramin al’amari ba ne, sakamakon zuwa da ya ke yi da haɗari iri daban-daban.

Wasu matan, bayan sun ɗauki ciki ne suke haɗuwa da cututtuka da dama; kamar ciwon zuciya, ciwon siga, hawan jini da sauran makamantansu. Don haka, a nan ya kamata a sani cewa; babu yadda za a yi mace ta ɗauki ciki ba tare da jikinta ya canza ba.

Wannan dalili ne ya sa, idan nauyin mai juna biyu bai kai yadda ake buƙata ba, sai a ja hankalinta ta yi wasu abubuwa da za su sa nauyin nata ya ƙaru, haka nan; idan nauyin nata ya yi yawa, musamman ga mata masu ƙiba; nan ma a kan ja hankalinsu su yi ƙoƙari wajen rage nauyin nasu.

ADVERTISEMENT

Saboda haka, da zarar an ce mace na da ciki; abubuwa da dama na sauya yanayin jikinta, wata ta ƙara ƙiba, wata ƙuraje su feso mata a fuska, wata kalar fatarta ta canja; wani wajen ya yi fari wani ya yi baƙi, wasu su yi ta samun ƙananan cututtuka, wasu amai, wasu kuma saboda damuwa su yi ta faman kuka ba tare da an yi musu komai ba.

Don haka, ya zama wajibi maza su riƙa yi wa matansu uzuri a yayin da suke ɗauke da juna biyu da kuma bayan sun haihu. Misali, babu yadda za a yi a ce mace ta ɗauki ciki tsawon wata tara tana tare da shi, sannan bayan ta haihu a kuma yi tunanin cewa; wannan ciki nata zai dawo kamar yadda yake a baya.

LABARAI MASU NASABA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

Har ila yau, maza da dama na da irin wannan ɗabi’a ta tsangwamar matansu, sakamakon yadda jikinsu yake sauyawa bayan sun haihu, musamman ganin yadda cikinsu yake yin shaida ko tattarewa ko kuma girma ta hanyar samun tumbi.

Irin wannan tsangwamar da maza ke yi wa mata, ko kaɗan bai dace ba; domin kuwa wasu matan na shiga cikin mummunan hali tare da takurawa kansu, ta hanyar kashe kuɗaɗensu don ganin sun samu maganin wannan matsala, wadda babu yadda za a yi a iya magance ta, tunda halittar ce a haka; kamar shekaru ne duk yadda za ka yi, babu wata dabara da za ta iya ɓoye su.

Saboda haka, mata ya kamata ku kiyaye; ku daina zuwa kuna kashe kuɗaɗenku babu gaira babu dalili, amma babu wani magani da za a baki ki sha tumbinki ya tafi, wasu sai su sha magani su je su yi ta zawo haka kawai, wai don tunbinsu ya ragu.

A nan, muna ƙara jan hankalin maza; su ji tsoron Allah su riƙa tausaya wa matayensu, musamman bayan sun samu juna biyu sun haihu. Sannan ku tuna cewa, wannan ciki da yake canja wa mata wasu ɓangarori na jikinsu, ku ne kuke yi musu ba daga gidajensu suke zuwa da shi ba.

Daga rumbun Dakta Na’ima Abubakar

Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

MASU ALAKA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
Ilimi

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Next Post
Sin Ta Kalubalanci Kwamitin Sulhun MDD Da Ya Gyara Ko Soke Takunkumin Da Aka Kakabawa Sudan Ta Kudu

Sin Ta Kalubalanci Kwamitin Sulhun MDD Da Ya Gyara Ko Soke Takunkumin Da Aka Kakabawa Sudan Ta Kudu

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.