ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Direbobi Sun Koka Kan Dawowar Matsalar Tsaro Kan Babbar Hanyar Damaturu Zuwa Biu

by Sani Anwar and Sulaiman
3 months ago
damaturu

Direbobi sun bukaci gwamnatin tarayya da Gwamnatin Jihar Borno, da su sake gina hanyar Damaturu zuwa Biu mai tsawon kilomita 85, wadda ta hada kananan hukumomi biyar a jihohin Yobe da Borno.

Mazauna yankin, sun nuna rashin jin dadinsu kan rashin kyawun hanyar, inda suka ce hakan ya janyo tsawaita lokacin tafiye-tafiye tare da tsananta matsalar tsaro. Kazalika, sun yi kira ga hukumomin tarayya da na jihohi da su gaggauta gyara hanyar, domin saukaka zirga-zirgar ababen hawa.

  • Indomie Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Al’adu A Bikin Kamun Kifi Na Argungu Karo Na 61
  • Bayan Shekaru 7, DSS Ta Sake Buɗe Binciken Ɓacewar Dadiyata 

A cewar matafiya da direbobi, lokacin tafiya kan babbar hanyar ya karu matuka daga kimanin sa’o’i biyu zuwa sama da sa’o’i shida, wanda hakan ya haifar da karuwar amfani da man fetur da yawan fashewar ababen hawa da kuma kara fuskantar hare-hare da sace-sacen ‘yan Boko Haram.

ADVERTISEMENT

Malam Bukar Mustapha, wani direban mota ya ce; masu ababen hawa, suna bin hanyar ne a kullum cikin fargabar sace su daga ’yan tada kayar baya da ke cin gajiyar rashin kyawun hanyar.

Daily trust ta rawaito cewa, sojoji na bincikar hanyar kowace safiya, domin gano ababen fashewa da ake zargi kafin su bar masu ababen hawa su tafi.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Wata fasinja mai suna Fatima Modu ta shaida wa Daily trust cewa, wasu ‘yan bindiga ne suka sace ‘yan’uwanta a kan hanya makwanni biyu da suka wuce.

“Duk da kasancewar wuraren bincike na jami’an tsaro, amma har yanzu akwai matsala, domin kuwa ana ci gaba da samun asarar rayuka da dama, mata masu juna biyu da ke tafiya asibitoci don haihuwa ko kula da lafiyarsu na fuskantar kalubale sosai,” in ji ta.

Wani direban mota, Yusha’u Umar ya ce; rashin kyawun titin na jawo wa direbobi asara mai dimbin yawa, sakamakon gyare-gyaren ababen hawansu, kamar fashewar tayoyi da sauran matsalolin inji.

“A da, muna shafe sa’o’i biyu kacal daga Damaturu zuwa Biu, amma yanzu muna kwashe sama da sa’o’i shida, lamarin ya aara ta’azzara matsalar rashin tsaro, saboda ‘yan tada kayar baya suna amfani da munanan hanyoyin wajen kai hare-hare,” in ji shi.

Shugaban kungiyar NURTW, reshen Damaturu, Mohammed Maina, ya bayyana hanyar a matsayin wata “mummunan hanya” don haka, ya bukaci gwamnati ta sake gina ta, domin kare afkuwar hadura da hare-hare kan masu ababen hawa.

Duk kokarin jin ta bakin babban kwamandan ayyuka na gwamnatin tarayya a Jihar Yobe, amma abin ya ci tura, sakamakon an ce ba ya jihar, ya je wani aiki da aka tura shi.

damaturu
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba
damaturu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
Rikicin Kabilanci A Jihar Ribas Ya Tayar Da Hankalin Al’umma

Rikicin Kabilanci A Jihar Ribas Ya Tayar Da Hankalin Al’umma

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.