An lalata kayayyaki na miliyoyin naira, biyo bayan zanga-zangar da ‘yan Arewa suka yi a garin Fatakwal, babban birnin Jihar Ribas, kan kisan wani mazaunin garin Igwuruta da ke Karamar Hukumar Ikwerre da ake zargin wani dan AcaBa ya yi.
An tattaro cewa, Nchelem Samuel Festus, dan asalin Igwuruta ne, wanda aka samu da laifin satar babur a wani shago mallakin ‘yan Arewa. Yayin da ake kokarin kwato babur din, an ce an caka masa wuka, inda daga bisani kuma ya mutu.
- Kisan Ƙare Dangi: Sojojin Amurka Sun Fara Aikin Samar Da Tsaro A Nijeriya
- Makomar Nijeriya Na Hannun FIFA – Shehu Dikko
Lamarin, wanda ya faru a ranar 10 ga watan Fabrairu, ya haifar da zanga-zanga, inda masu zanga-zangar ke zargin cewa; ‘yan Arewa ne da ke sana’ar tuka babur (AcaBa) ke da alhakin mutuwar ta Festus.
Har ila yau, masu zanga-zangar, sun ci gaba da zargin ’yan Arewar da hannu a wasu laifuka da suka hada da fyade da kuma garkuwa da mutane.
Rikicin dai, ya ta’azzara ne yayin da matasa suka tare titin filin jirgin sama na Fatakwal, inda suka bukaci da a gaggauta dakatar da zirga-zirgar ‘yan AcaBa daga Arewa a yankin.
Sun kuma yi kira da a rufe wuraren zubar da shara da ake zargin ’yan Arewan, a kuma kama tare da hukunta wadanda ke da hannu a kisan na Festus, da kuma hana makiyaya shiga gonakin mutane da suke yi.
Masu zanga-zangar, sun bayar da wa’adin sa’o’i 48 ga hukumomin tsaro, inda suka yi gargadin cewa; rashin biyan bukatunsu na iya tilastawa al’umma daukar matakan kare rayuka da dukiyoyi, tare da tabbatar da cewa; matakin nasu zai kasance a cikin tsarin doka da oda.
Tashin hankalin ya yi kamari ne a ranar Asabar da ta gabata, yayin da wani mai tura Baro, mai suna Zakara Afaaruwu ya daBa wa wani dan kasuwa mai suna Higightor Wenem daga Jihar Benuwe wuka har lahira, a lokacin da suke takaddama a Fatakwal.
Lamarin dai ya haifar da wani sabon rikici, wanda ya kai ga sake kai hare-hare a kan ‘yan kasuwar Arewacin kasar a Igwuruta, inda aka yi ta’adi a wasu kasuwanni tare da yin sace-sace.
“Kada ku danganta ’yan Arewa da wasu keBantattun laifuka.”
Shugaban al’ummar Hausawa a Jihar Ribas, Malam Musa Saidu, ya bayyana matukar bakin cikinsa, kan kashe-kashen da aka yi, ya kuma yi gargadin a guji alakanta aikata laifuka da al’ummar Hausawa ko wata kabila daban.
Ya ce, “An samu rashin fahimtar juna ne a tsakanin wani yaro dan Arewa da kuma wani dan garin Igwuruta, wanda abin takaici ya yi sanadin mutuwar wasu mutane, kamar yadda ni ma na samu bayani, saboda ni kaina ban je wurin ba, an ce; yaron Arewan ya daBa wa yaron garin wuka, har ya mutu, hakan ya sa aka yi wannan zanga-zanga, amma zanga-zangar ita ce; ta Hausawa su fita daga garin, idan wani ya yi laifi, hukuma ce ya kamata ta kama shi, jami’an tsaro su gurfanar da shi, amma mene ne dalilin yin zanga-zanga tare da neman Hausawa su bar garin?
“Rokona ga ’yan’uwanmu maza da mata a Jihar Ribas, ‘yan asalin jihar da wadanda ba ‘yan asalin jihar ba shi ne, mu yi hakuri da abin da ya faru, mu ba masu tayar da hankali ba ne, duk wanda ya aikata laifi doka ta dauki mataki akansa, yin zanga-zangar adawa da al’umma gaba-daya tamkar kiyayya ce, kuma kiyayya na iya haifar da karin tashin hankali,” in ji shi.















Discussion about this post