ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Kabilanci A Jihar Ribas Ya Tayar Da Hankalin Al’umma

by Sani Anwar and Sulaiman
4 months ago
Ribas

An lalata kayayyaki na miliyoyin naira, biyo bayan zanga-zangar da ‘yan Arewa suka yi a garin Fatakwal, babban birnin Jihar Ribas, kan kisan wani mazaunin garin Igwuruta da ke Karamar Hukumar Ikwerre da ake zargin wani dan AcaBa ya yi.

An tattaro cewa, Nchelem Samuel Festus, dan asalin Igwuruta ne, wanda aka samu da laifin satar babur a wani shago mallakin ‘yan Arewa. Yayin da ake kokarin kwato babur din, an ce an caka masa wuka, inda daga bisani kuma ya mutu.

  • Kisan Ƙare Dangi: Sojojin Amurka Sun Fara Aikin Samar Da Tsaro A Nijeriya
  • Makomar Nijeriya Na Hannun FIFA – Shehu Dikko

Lamarin, wanda ya faru a ranar 10 ga watan Fabrairu, ya haifar da zanga-zanga, inda masu zanga-zangar ke zargin cewa; ‘yan Arewa ne da ke sana’ar tuka babur (AcaBa) ke da alhakin mutuwar ta Festus.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, masu zanga-zangar, sun ci gaba da zargin ’yan Arewar da hannu a wasu laifuka da suka hada da fyade da kuma garkuwa da mutane.

Rikicin dai, ya ta’azzara ne yayin da matasa suka tare titin filin jirgin sama na Fatakwal, inda suka bukaci da a gaggauta dakatar da zirga-zirgar ‘yan AcaBa daga Arewa a yankin.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Sun kuma yi kira da a rufe wuraren zubar da shara da ake zargin ’yan Arewan, a kuma kama tare da hukunta wadanda ke da hannu a kisan na Festus, da kuma hana makiyaya shiga gonakin mutane da suke yi.

Masu zanga-zangar, sun bayar da wa’adin sa’o’i 48 ga hukumomin tsaro, inda suka yi gargadin cewa; rashin biyan bukatunsu na iya tilastawa al’umma daukar matakan kare rayuka da dukiyoyi, tare da tabbatar da cewa; matakin nasu zai kasance a cikin tsarin doka da oda.

Tashin hankalin ya yi kamari ne a ranar Asabar da ta gabata, yayin da wani mai tura Baro, mai suna Zakara Afaaruwu ya daBa wa wani dan kasuwa mai suna Higightor Wenem daga Jihar Benuwe wuka har lahira, a lokacin da suke takaddama a Fatakwal.

Lamarin dai ya haifar da wani sabon rikici, wanda ya kai ga sake kai hare-hare a kan ‘yan kasuwar Arewacin kasar a Igwuruta, inda aka yi ta’adi a wasu kasuwanni tare da yin sace-sace.

“Kada ku danganta ’yan Arewa da wasu keBantattun laifuka.”

Shugaban al’ummar Hausawa a Jihar Ribas, Malam Musa Saidu, ya bayyana matukar bakin cikinsa, kan kashe-kashen da aka yi, ya kuma yi gargadin a guji alakanta aikata laifuka da al’ummar Hausawa ko wata kabila daban.

Ya ce, “An samu rashin fahimtar juna ne a tsakanin wani yaro dan Arewa da kuma wani dan garin Igwuruta, wanda abin takaici ya yi sanadin mutuwar wasu mutane, kamar yadda ni ma na samu bayani, saboda ni kaina ban je wurin ba, an ce; yaron Arewan ya daBa wa yaron garin wuka, har ya mutu, hakan ya sa aka yi wannan zanga-zanga, amma zanga-zangar ita ce; ta Hausawa su fita daga garin, idan wani ya yi laifi, hukuma ce ya kamata ta kama shi, jami’an tsaro su gurfanar da shi, amma mene ne dalilin yin zanga-zanga tare da neman Hausawa su bar garin?

“Rokona ga ’yan’uwanmu maza da mata a Jihar Ribas, ‘yan asalin jihar da wadanda ba ‘yan asalin jihar ba shi ne, mu yi hakuri da abin da ya faru, mu ba masu tayar da hankali ba ne, duk wanda ya aikata laifi doka ta dauki mataki akansa, yin zanga-zangar adawa da al’umma gaba-daya tamkar kiyayya ce, kuma kiyayya na iya haifar da karin tashin hankali,” in ji shi.

Ribas
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tinubu Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Kan Jajircewarsu Wajen Kawo Karshen Ta’addanci
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
Ribas
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
  • Sulaiman
    Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
  • Sulaiman
    Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

MASU ALAKA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
Rahotonni

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati
Labarai

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare
Labarai

Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

June 12, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Da Gwamnonin APC Sun Ba Da Gudummawar Naira Biliyan 8 Ga ‘Yan Kasuwar Singa

Gwamnatin Tarayya Da Gwamnonin APC Sun Ba Da Gudummawar Naira Biliyan 8 Ga ‘Yan Kasuwar Singa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.