ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Kabilanci A Jihar Ribas Ya Tayar Da Hankalin Al’umma

by Sani Anwar and Sulaiman
5 months ago
Ribas

An lalata kayayyaki na miliyoyin naira, biyo bayan zanga-zangar da ‘yan Arewa suka yi a garin Fatakwal, babban birnin Jihar Ribas, kan kisan wani mazaunin garin Igwuruta da ke Karamar Hukumar Ikwerre da ake zargin wani dan AcaBa ya yi.

An tattaro cewa, Nchelem Samuel Festus, dan asalin Igwuruta ne, wanda aka samu da laifin satar babur a wani shago mallakin ‘yan Arewa. Yayin da ake kokarin kwato babur din, an ce an caka masa wuka, inda daga bisani kuma ya mutu.

  • Kisan Ƙare Dangi: Sojojin Amurka Sun Fara Aikin Samar Da Tsaro A Nijeriya
  • Makomar Nijeriya Na Hannun FIFA – Shehu Dikko

Lamarin, wanda ya faru a ranar 10 ga watan Fabrairu, ya haifar da zanga-zanga, inda masu zanga-zangar ke zargin cewa; ‘yan Arewa ne da ke sana’ar tuka babur (AcaBa) ke da alhakin mutuwar ta Festus.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, masu zanga-zangar, sun ci gaba da zargin ’yan Arewar da hannu a wasu laifuka da suka hada da fyade da kuma garkuwa da mutane.

Rikicin dai, ya ta’azzara ne yayin da matasa suka tare titin filin jirgin sama na Fatakwal, inda suka bukaci da a gaggauta dakatar da zirga-zirgar ‘yan AcaBa daga Arewa a yankin.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sun kuma yi kira da a rufe wuraren zubar da shara da ake zargin ’yan Arewan, a kuma kama tare da hukunta wadanda ke da hannu a kisan na Festus, da kuma hana makiyaya shiga gonakin mutane da suke yi.

Masu zanga-zangar, sun bayar da wa’adin sa’o’i 48 ga hukumomin tsaro, inda suka yi gargadin cewa; rashin biyan bukatunsu na iya tilastawa al’umma daukar matakan kare rayuka da dukiyoyi, tare da tabbatar da cewa; matakin nasu zai kasance a cikin tsarin doka da oda.

Tashin hankalin ya yi kamari ne a ranar Asabar da ta gabata, yayin da wani mai tura Baro, mai suna Zakara Afaaruwu ya daBa wa wani dan kasuwa mai suna Higightor Wenem daga Jihar Benuwe wuka har lahira, a lokacin da suke takaddama a Fatakwal.

Lamarin dai ya haifar da wani sabon rikici, wanda ya kai ga sake kai hare-hare a kan ‘yan kasuwar Arewacin kasar a Igwuruta, inda aka yi ta’adi a wasu kasuwanni tare da yin sace-sace.

“Kada ku danganta ’yan Arewa da wasu keBantattun laifuka.”

Shugaban al’ummar Hausawa a Jihar Ribas, Malam Musa Saidu, ya bayyana matukar bakin cikinsa, kan kashe-kashen da aka yi, ya kuma yi gargadin a guji alakanta aikata laifuka da al’ummar Hausawa ko wata kabila daban.

Ya ce, “An samu rashin fahimtar juna ne a tsakanin wani yaro dan Arewa da kuma wani dan garin Igwuruta, wanda abin takaici ya yi sanadin mutuwar wasu mutane, kamar yadda ni ma na samu bayani, saboda ni kaina ban je wurin ba, an ce; yaron Arewan ya daBa wa yaron garin wuka, har ya mutu, hakan ya sa aka yi wannan zanga-zanga, amma zanga-zangar ita ce; ta Hausawa su fita daga garin, idan wani ya yi laifi, hukuma ce ya kamata ta kama shi, jami’an tsaro su gurfanar da shi, amma mene ne dalilin yin zanga-zanga tare da neman Hausawa su bar garin?

“Rokona ga ’yan’uwanmu maza da mata a Jihar Ribas, ‘yan asalin jihar da wadanda ba ‘yan asalin jihar ba shi ne, mu yi hakuri da abin da ya faru, mu ba masu tayar da hankali ba ne, duk wanda ya aikata laifi doka ta dauki mataki akansa, yin zanga-zangar adawa da al’umma gaba-daya tamkar kiyayya ce, kuma kiyayya na iya haifar da karin tashin hankali,” in ji shi.

Ribas
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnati Ta Amince Da Inganta Cibiyar Kula Da Saran Maciji A Gwambe
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Hukumar NDLEA Ta Lalata Sama Da Tan 12 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
Ribas
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI
  • Sulaiman
    Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

MASU ALAKA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA
Labarai

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi
Manyan Labarai

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Da Gwamnonin APC Sun Ba Da Gudummawar Naira Biliyan 8 Ga ‘Yan Kasuwar Singa

Gwamnatin Tarayya Da Gwamnonin APC Sun Ba Da Gudummawar Naira Biliyan 8 Ga ‘Yan Kasuwar Singa

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.