ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dokar Hana Aikin Tilas Ko Dokar Neman Durkusar Da Tattalin Arzikin Sin?

by CMG Hausa
4 years ago
xinjiang

Amurka ta fara amfani da dokar da ta zartar dake ikirarin hana aikin tilas a jihar Xinjiang ta kasar Sin a jiya.

Dokar na nufin kin karbar kayayyakin da aka samar a jihar, har sai an gabatar da shaidun dake tabbatar da cewa, ba ta hanyar aikin tilas aka samar da su ba.

  • Sin Tana Adawa Da Dokar Hana Kayayyakin Da Suka Shafi Jihar Xinjiang Shiga Amurka

Rahotanni sun nuna cewa, Xinjiang ce ke samar da kaso 20 na audugar da ake amfani da ita a duniya. Kuma a lokacin girbin auduga, ba al’ummar jihar kadai ba, har wasu daga sauran sassan kasar Sin na zuwa Xinjiang domin gudanar da aiki don samun karin kudin shiga. Shin idan har da gaske aikin tilas suke yi, me ya sa wasu za su niki gari su tafi inda ake aikin tilas? Wannan ikirari na Amurka na tattare da ayoyin tambaya.

ADVERTISEMENT

Sanin kowa ne cewa, rashin aikin yi, shi ne tushen rikici a yankuna daban daban. A ganina, ban da saurin ci gaban tattalin arzikin Sin mai juriya da ya tsonewa Amurka ido, akwai ma zaman lafiya da kasar ke morewa da kuma ammana da gwamnati da al’ummarta suka yi, wanda ya yi hannun riga da yanayin Amurka.

Kullum Amurka da kawayenta na yayata batun kare hakkin dan Adam a jihar Xinjiang, amma abubuwan da take yi ba sa dacewa da furucinta. Wannan doka a ganina, wani yunkuri ne na dankwafe ci gaban tattalin arzikin Sin da ma musgunawa al’ummar Xinjiang da take ikirarin karewa. Tun da noman auduga jigo ne a jihar Xinjiang, me zai faru idan aka daina sayen audugar a duniya? Wannan ba shi ne keta hakkin bil adama ba? Wato toshe musu hanyar samun kudin shiga, da zai shafi walwalarsu da yanayin zaman takewa.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Kamata ya yi Amurka ta zartar da dokokin da za su amfani al’ummarta kamar na hana mallakar bindiga da yaki da annobar COVId-19 da tunkarar matsalar tashin farashin kayayyaki, ba zartar da dokokin kan kayayyakin Sin ba.

Wannan mataki na Amurka, ba kamfanonin Xinjiang za su shafa kadai ba, har da kamfanonin Amurkar. Idan Amurka ba ta duba halin da za ta jefa ma’aikata da kamfanonin Sin ba, ai ya kamata ta duba na al’ummarta idan har ta damu da su.

An riga an shaida cewa, tubalin karfin tattalin arzikin kasar Sin ne samun gagarumar gudunmawa daga kasuwar cikin gida saboda yawan al’ummarta. Kana ba Amurka ce kadai ke cinikayya da Sin ba, don haka, matakin ita da al’ummarta zai fi yi wa tasiri ba kasar Sin. (Faeza Mustapha)

xinjiang
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
‘Yan Majalisar APC Takwas Sun Sauya Sheka Zuwa PDP A Jihar Kebbi

Adamu Yana Ganawar Sirri Da Sanatocin Da Za Su Yi Wa Jam'iyyar APC Takara

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.