ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dokar Hana Aikin Tilas Ko Dokar Neman Durkusar Da Tattalin Arzikin Sin?

by CMG Hausa
4 years ago
xinjiang

Amurka ta fara amfani da dokar da ta zartar dake ikirarin hana aikin tilas a jihar Xinjiang ta kasar Sin a jiya.

Dokar na nufin kin karbar kayayyakin da aka samar a jihar, har sai an gabatar da shaidun dake tabbatar da cewa, ba ta hanyar aikin tilas aka samar da su ba.

  • Sin Tana Adawa Da Dokar Hana Kayayyakin Da Suka Shafi Jihar Xinjiang Shiga Amurka

Rahotanni sun nuna cewa, Xinjiang ce ke samar da kaso 20 na audugar da ake amfani da ita a duniya. Kuma a lokacin girbin auduga, ba al’ummar jihar kadai ba, har wasu daga sauran sassan kasar Sin na zuwa Xinjiang domin gudanar da aiki don samun karin kudin shiga. Shin idan har da gaske aikin tilas suke yi, me ya sa wasu za su niki gari su tafi inda ake aikin tilas? Wannan ikirari na Amurka na tattare da ayoyin tambaya.

ADVERTISEMENT

Sanin kowa ne cewa, rashin aikin yi, shi ne tushen rikici a yankuna daban daban. A ganina, ban da saurin ci gaban tattalin arzikin Sin mai juriya da ya tsonewa Amurka ido, akwai ma zaman lafiya da kasar ke morewa da kuma ammana da gwamnati da al’ummarta suka yi, wanda ya yi hannun riga da yanayin Amurka.

Kullum Amurka da kawayenta na yayata batun kare hakkin dan Adam a jihar Xinjiang, amma abubuwan da take yi ba sa dacewa da furucinta. Wannan doka a ganina, wani yunkuri ne na dankwafe ci gaban tattalin arzikin Sin da ma musgunawa al’ummar Xinjiang da take ikirarin karewa. Tun da noman auduga jigo ne a jihar Xinjiang, me zai faru idan aka daina sayen audugar a duniya? Wannan ba shi ne keta hakkin bil adama ba? Wato toshe musu hanyar samun kudin shiga, da zai shafi walwalarsu da yanayin zaman takewa.

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Kamata ya yi Amurka ta zartar da dokokin da za su amfani al’ummarta kamar na hana mallakar bindiga da yaki da annobar COVId-19 da tunkarar matsalar tashin farashin kayayyaki, ba zartar da dokokin kan kayayyakin Sin ba.

Wannan mataki na Amurka, ba kamfanonin Xinjiang za su shafa kadai ba, har da kamfanonin Amurkar. Idan Amurka ba ta duba halin da za ta jefa ma’aikata da kamfanonin Sin ba, ai ya kamata ta duba na al’ummarta idan har ta damu da su.

An riga an shaida cewa, tubalin karfin tattalin arzikin kasar Sin ne samun gagarumar gudunmawa daga kasuwar cikin gida saboda yawan al’ummarta. Kana ba Amurka ce kadai ke cinikayya da Sin ba, don haka, matakin ita da al’ummarta zai fi yi wa tasiri ba kasar Sin. (Faeza Mustapha)

xinjiang
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
Daga Birnin Sin

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
Daga Birnin Sin

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Next Post
‘Yan Majalisar APC Takwas Sun Sauya Sheka Zuwa PDP A Jihar Kebbi

Adamu Yana Ganawar Sirri Da Sanatocin Da Za Su Yi Wa Jam'iyyar APC Takara

LABARAI MASU NASABA

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.