ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Editan Leadership Ya Rubuta Littafi Kan Sauyin Zamani A Aikin Jarida

by Abubakar Sulaiman
2 weeks ago

Babban Editan Labarai na rukunin kamfanin jaridar LEADERSHIP, Dr. Sunday Isuwa, ya wallafa wani sabon littafi mai taken “Digital Shift In Nigeria’s Newspaper Industry”, wanda ya yi fashin baƙi kan yadda ci gaban fasaha ke sauya fasalin yadda ake gudanar da aikin jarida, tsarin kasuwanci, da kuma yadda kafafen yaɗa labarai ke cuɗanya da masu karatunsu a Nijeriya.

A cewar wata sanarwa da aka fitar, za a ƙaddamar da wannan muhimmin littafi a hukumance a ranar 29 ga watan Oktobar 2026, da misalin karfe 10:00 na safe a Babban Zauren Taro na Jami’ar NOUN, da ke Jabi, a birnin Tarayya Abuja.

Tsohon Kakakin Majalisar Wakilai, Honarabul Yakubu Dogara, wanda kuma shi ne Shugaban Kamfanin Ba da Lamuni na Ƙasa (NCGC), ne zai kasance shugaban taron, yayin da Mataimakin Shugaban Jami’ar NOUN, Farfesa Uduma Oji Uduma zai yi sharhin littafin. Farfesa Rotimi Olatunji, malami a Jami’ar Jihar Legas kuma shugaban ƙungiyar Malaman Sadarwa ta Kasa, shi ne ya rubuta gabatarwar (foreword) littafin.

ADVERTISEMENT

Manyan masana da ƙwararru a fagen aikin jarida sun yi matuƙar yaba wa wannan aiki. Farfesa Umaru Pate na Jami’ar Bayero ta Kano ya siffanta littafin a matsayin wanda ya zo a daidai lokacin da ake buƙatar fahimtar irin sauye-sauyen da ke faruwa a masana’antar yaɗa labarai, inda ya bayyana cewa littafin ya taɓo muhimman batutuwa kamar tattara labarai ta amfani da kafofin sadarwa na zamani da kuma yaƙi da labaran karya.

Haka zalika, Farfesa Farooq Kperogi na Jami’ar Kennesaw da ke ƙasar Amurka ya bayyana cewa Dr. Isuwa ya yi amfani da kwarewarsa a aikin jarida da kuma bincike na ilimi wajen fito da yadda jaridun gargajiya suka koma kan tsarin intanet.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

A nasa jawabin, Manajan Darakta na Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN), Malam Ali M. Ali, ya roƙi dukkanin ƙwararru, da malamai, da masu tsara manufofi da su halarci wannan taron ƙaddamarwa.

Ya nuna cewa littafin bai tsaya kawai wajen bayyana tarihin jaridu a Nijeriya ba, har ma ya duba ƙalubalen da ‘yan jarida ke fuskanta wajen daidaita gaggawar fitar da labari da kuma tabbatar da sahihancinsa a wannan zamanin da fasaha ta mamaye komai, wanda hakan zai taimaka wajen samar da madogara ta gari ga ɗalibai da masu nazarin aikin jarida a ƙasar nan.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Kasar Sin Na Samar Da Kyakkyawar Fata Ga Al’ummar Afrika

Kasar Sin Na Samar Da Kyakkyawar Fata Ga Al’ummar Afrika

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.