Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta EFCC ta ayyana tsohuwar Ministar Harkokin Jin-ƙai, Agaji da Ci gaban Jama’a, Sadiya Umar Farouq, a matsayin wacce ake nema ruwa a jallo bisa zargin cin amanar aiki da karkatar da kuɗaɗen gwamnati.
A cikin wata sanarwa da hukumar ta wallafa, EFCC ta buƙaci duk wanda ke da bayanai kan inda take da ya tuntubi ofisoshinta a faɗin ƙasar nan. Hukumar ta ce Sadiya Farouq ‘yar asalin jihar Zamfara ce mai shekara 52, kuma adireshinta na ƙarshe da aka sani shi ne EN008, Okpo River, kusa da Agulu Street a Maitama, Abuja.
Sadiya Farouq ta riƙe muƙamin minista tsakanin shekarar 2019 zuwa 2023 a gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari. EFCC na binciken zargin almundahanar kuɗi har Naira biliyan 37 da ake alaƙantawa da ma’aikatar a lokacin da take jagoranci.
Rahotanni sun bayyana cewa a ranar 16 ga Afrilu, 2026, wata babbar kotun tarayya da ke Apo a Abuja ta bayar da sammacin kama ta tare da Bashir Nura Alkali, babban sakatare a ma’aikatar, bayan sun gaza bayyana a kotu domin fara shari’a.
Ana tuhumar su tare da wani Sani Mohammed da laifuka guda 21 da suka haɗa da cin amanar aiki da amfani da ofis ba bisa ƙa’ida ba. EFCC ta yi zargin cewa sun karkatar da dala miliyan 1.3 da kuma Naira miliyan 746.6 daga kuɗaɗen da aka mayar wa ma’aikatar ƙarƙashin wani shirin tallafin jama’a domin amfanin kansu.















Discussion about this post