ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

El-Rufai Zai Amsa Goron Gayyatar EFCC A Ranar Litinin — Lauyansa

by Sadiq
7 months ago
El-Rufai

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, zai amsa goron gayyatar da Hukumar Yaƙi da Masu Yi wa Tattalin Arzikin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC) da misalin ƙarfe 10 na safiyar ranar Litinin.

Lauyansa, Ubong Esop Akpan ne, ya bayyana hakan a ranar Alhamis yayin da yake mayar da martani kan rahotanni cewa jami’an tsaro sun yi ƙoƙarin kama El-Rufai a Filin Jirgin Saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja.

  • Gwamnatin Kano Ta Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Hana Kwankwaso Shigowa Kano — Buba Galadima 
  • Jami’an Tsaro Sun Ƙwace Fasfon El-Rufai A Filin Jirgin Saman Abuja – Hadimi

A cewar lauyan, jami’an tsaro sun tunkari El-Rufai ne da yammacin ranar Alhamis bayan ya dawo daga birnin Alkahira na ƙasar Masar, a cikin jirgin EgyptAir.

ADVERTISEMENT

Mista Akpan ya ce EFCC ta aike da wasiƙar gayyata zuwa gidan El-Rufai lokacin da yake ƙasar waje, don haka ba zai yiwu ya amsa gayyatar nan take ba.

Ya ƙara da cewa tun a watan Disamban 2025 suka sanar da EFCC cewa El-Rufai zai samu damar zuwa hukumar sai ya dawo Najeriya.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ya ce sun bayyana a fili cewa zai je ofishin EFCC da misalin ƙarfe 10 na safiyar ranar Litinin, 16 ga watan Fabrairu, 2026.

Lauyan ya ce duk wani yunƙurin kama shi duk da ya amince zai je da kansa, bai dace ba kuma ya saɓa wa tsarin doka.

Haka kuma ya buƙaci a dawo masa da fasfo ɗinsa, wanda ya ce an karɓe shi a lokacin da lamarin ya faru a filin jirgin saman Abuja.

Zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, EFCC ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance kan batun ba.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Ministan Wajen Nijeriya Ya Fitar Da Mukalar Taya Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Nijeriya Da Sin

Ministan Wajen Nijeriya Ya Fitar Da Mukalar Taya Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Nijeriya Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.