Fadar Shugaban Ƙasa ta buƙaci a yi cikakken bincike a kan tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, na cewa an yi kutse a wayar Nuhu Ribadu tare da sauraron kiran wayarsa.
El-Rufai ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi da gidan talabijin a ranar Juma’a.
- An Gabatar Da Bikin Share Fagen Shirin Talibijin Na Murnar Sabuwar Shekarar Sinawa A Masar
- Jihar Oyo Za Ta Sayo Laftof 60,000 Saboda Sabon Tsarin Jarrabawa
Ya ce yana da labarin yunƙurin kama shi da aka yi lokacin da ya sauka a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe a ranar Alhamis.
Ya zargi Ribadu da bayar da umarnin kama shi, yana mai cewa ya ji kiran wayar da aka yi saboda an yi kutse a wayar.
Sai dai kakakin shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya ce maganar El-Rufai laifi ce.
Ya kuma tambayi ko shi da mutanensa suna da hurumin yin hakan.
Onanuga ya jaddada cewa dole ne a binciki lamarin sosai, kuma duk wanda aka samu da laifi a hukunta shi, domin babu wanda ya fi ƙarfin doka.















Discussion about this post