Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta yi tir da kakkausan harshe tare da bayyana damuwarta kan kisan gilla da ƙona wata mata ƙurmus da wasu fusatattun matasa suka yi a yankin Marabar Jos, sakamakon zargin satar yara da ba a tabbatar ba.
Kakakin rundunar, DSP Mansir Hassan, ne ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa, inda ya bayyana lamarin a matsayin abin baƙin ciki, da rashin tausayi, da kuma karan tsaye ga tsarin doka.
Bayanai sun nuna cewa, da misalin ƙarfe 10:00 na safe ne jami’an tsaro ƙarƙashin babban jami’in ƴansanda na yankin (DPO) suka ceci matar daga hannun dandazon jama’ar da suka far mata, inda aka kai ta ofishin ‘yansanda domin bata kariya da fara gudanar da bincike kan zargin da ake mata. Sai dai, daga baya ɗaruruwan mazauna yankin sun dira ofishin ‘yansandan.
Fusatattun mutanen sun yi amfani da yawansu wajen fito da matar ta karfin tsiya daga hannun jami’an tsaro, inda suka yi mata dukan kawo wuƙa har ta ce ga garinku nan, sannan suka banka wa gawar tata wuta ta ƙone ƙurmus. Ƙungiyoyin kare haƙƙin bil’adama, ciki har da Amnesty International, sun bayyana matar a matsayin Malama Ummulkhairi, mahaifiyar yara biyar, sannan sun yi kira da a gudanar da bincike mai zaman kansa kan lamarin.
Daga karshe, rundunar ‘yansandan ta tabbatar da cewa an riga an kama wasu daga cikin matasan da ake zargi da hannu a wannan ɗanyen aiki, kuma ana ci gaba da farautar sauran waɗanda suka gudu. Kwamishinan ‘yansandan jihar ya gargaɗi jama’a cewa babu wani mutum ko ƙungiyar da ke da ikon ɗaukar doka a hannunsa, kuma za a gurfanar da dukkan waɗanda aka kama gaban kotu domin fuskantar hukunci mai tsanani.












Discussion about this post