ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fursunoni 53,836 Ke Jiran Shari’a Don Sanin Matsayinsu A Gidajen Gyaren Hali A Nijeriya

by Muhammad
2 years ago
Fursunoni

Hukumar Kula da gidajen gyaran hali ta Nijeriya (NCoS) ta ce, akalla fursunoni 53, 836 a gidajen gyaran hali 253 ne ake tsare da su a fadin kasar nan suna dakon jiran shari’a a lissafin da ke kasa a ranar 18,ga Disambar 2023.

Mai magana da yawun hukumar, Mataimakin Kwanturola (ACC) Abubakar Umar ne ya shaida wa manema Labarai a Abuja ranar Alhamis.

  • Hukumar Da Ke Kula Da Gidajen Yarin Nijeriya Na Cigiyar Fursunoni 69 Da Suka Tsere Daga Kuje
  • Gwamnatin Tarayya Na Kashe Miliyan 3 Kullum Wajen Ciyar da Fursunoni 4,000 – Minista

Umar ya ce, takaita fursunoni a fadin kasar nan ta hanyar yanke musu hukunci da kuma wadanda ke jiran tuhuma sun kai 77,849.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, jimillar fursunoni 24, 013 “ya kara da cewa fursunonin maza da aka yankewa hukuncin sun kai 23,569 da mata 444.

“Kididdigar ta nuna cewa kashi 69 cikin 100 na fursunonin da ake tsare da su a gidajen gyaren hali da ake tsare da su suna jiran shari’a, yayin da kashi 31 cikin 100 na fursunonin aka yanke musu hukunci,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Umar ya ce daya daga cikin kalubalen da hukumar ke fuskanta shi ne batun rugujewar gine-ginen da ke haifar da cunkoso a cikin gidajen gyaren halin da ke kasar nan.

Ya ce, kwanan nan gwamnati ta gina ƙarin wuraren ajiya na zamani guda 3,000 a shiyyoyin Nijeriya shida don rage cunkoso a gidajen gyaren halin da ake da su.

Ya ce, shirin zai taimaka wajen rage cunkoso a cibiyoyin tare da inganta walwala da lafiyar fursunonin.

“An kaddamar da na Kano kuma muna sa ran kammalawa cikin gaggawa da sanya sauran kayayyakin da ake bukata,” in ji shi.

Ya kara da cewa “aikin da ake yi na Abuja da da Portharcourt ana dab da kammalawa kuma nan ba da jimawa ba za a kaddamar da su.”

Ya kuma yabawa Gwamnatin Tarayya kan tara naira miliyanN585 don biyan tarar fursunoni a wani yunkuri na rage cinkoso a gidajen gyaran hali da ke a fadin kasar nan.

Ya kuma yaba da kokarin gwamnatin tarayya na sakin fursunoni 4,068 da ke zaman gidan gyaren hali daban-daban a kasar nan.

Fursunoni
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
Kotun Daukaka Karar Zaben Gwamnan Kano Za Ta Sanar Da Ranar Yanke Hukunci Kan Shari’ar

Kotun Ƙoli Ta Kammala Sauraron Ƙarar Zaɓen Kano, Za Ta Sanar Da Ranar Yanke Hukunci

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.