ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

GDPn Nijeriya Ya Yi Ƙasa Fiye da Na Shekaru 20 da Suka Wuce A Zamanin Obasanjo — Hashim

by Bello Hamza and Sulaiman
4 months ago
Hashim

Wani ɗan takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Dr. Gbenga Hashim, ya soki yadda tattalin arzikin Nijeriya ke tafiya a ƙarƙashin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, yana mai cewa tattalin arzikin ƙasar ya fi rauni a yau idan aka kwatanta da lokacin mulkin tsofaffin shugabanni, musamman Olusegun Obasanjo da Goodluck Jonathan.

 

Hashim ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin wata tattaunawa kai tsaye a tashar Channels Television tare da Seun Okinbaloye, inda suka tattauna kan makomar tattalin arzikin Najeriya da kuma rawar da matasan Najeriya ke takawa a tattalin arzikin duniya, a shirin Politics Today.

ADVERTISEMENT
  • Kotun Amurka Ta Yanke Wa Wanda Yayi Yunƙurin Kashe Trump Hukuncin Ɗaurin Rai Da Rai
  • INEC Ta Amince Da Shugabancin PDP Tsagin Wike

Ya ce bayanan tattalin arziki na hukuma sun nuna cewa tsare-tsaren kuɗi da na kasafin kuɗi na gwamnatocin jam’iyyar APC a cikin shekaru goma da suka gabata sun gaza tafiya daidai da karuwar yawan jama’a da buƙatun ci gaba.

 

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

“GDP a zamanin Obasanjo ya kai kusan dala biliyan 267. A zamanin Jonathan kuwa ya tashi zuwa sama da dala biliyan 574. Amma a yau, a ƙarƙashin Tinubu, ya faɗi zuwa kusan dala biliyan 230. Wannan koma baya ne mai tayar da hankali ga ƙasa mai yalwar albarkatun ɗan Adam da na ƙasa,” in ji Hashim.

 

Ɗan takarar na PDP ya kuma nuna damuwa kan faduwar darajar naira, yana mai cewa darajar da take da ita a halin yanzu ta yi ƙasa ƙwarai da abin da ya dace da tushen tattalin arzikin Najeriya. Ya ce hakan ya ƙara tsadar rayuwa tare da raunana gwiwar masu zuba jari.

 

Hashim, wanda shi ma ɗan kasuwa ne a matakin duniya, ya kuma tambayi irin gudunmawar da Shugaba Tinubu ya bayar wajen ci gaban jihar Lagos, yana kwatanta ta da ta tsohon shugaban soja, Janar Ibrahim Babangida (IBB). Ya ce Babangida ya fi bayar da gudunmawa mai ɗorewa ta hanyar gina Gadar Third Mainland.

 

“IBB ya fi ba da gudunmawa ga ci gaban Lagos saboda shi ne ya gina Gadar Third Mainland. Idan ka cire wannan gada a yau, me ya rage? Ƙaramar gadar Lekki da Tinubu ya gina kuma ya sanya kuɗin wucewa ba ta kai Third Mainland da IBB ya gina ba,” in ji Hashim.

 

Ya kuma yi watsi da jam’iyyar Action Democratic Congress (ADC) a matsayin wata sahihiyar madadin siyasa, yana cewa da dama daga cikin mambobinta suna da alaƙa da matsalolin tsaro da tattalin arziki da ƙasar ke fuskanta.

 

“Baya ga Peter Obi da watakila Atiku Abubakar, yawancin sauran ’yan ADC Buharawa ne da ake zargi da kasancewa cikin matsalar da muke ciki a yau,” in ji shi.

Hashim ya kalubalanci mambobin tawagar kula da tattalin arzikin gwamnatin Tinubu, ciki har da Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) da Ministan Kuɗi, da su fito fili su kare ayyukansu a muhawarar kai tsaye.

 

“Kalubale ne a fili — su fito da ƙwararrunsu, gwamnan CBN da ministan kuɗi, mu yi muhawara kai tsaye kan tattalin arziki,” in ji shi.

Yana mai jaddada cewa an rage darajar naira fiye da kima, Hashim ya ce karin yawan man fetur da ake samarwa daga kusan ganga 900,000 a rana zuwa kusan ganga miliyan 1.8, tare da raguwar shigo da man fetur sakamakon ƙarin tacewa a cikin gida, ya kamata su taimaka wajen ƙarfafa darajar naira, ba wai ta ci gaba da faduwa ba idan aka kwatanta da zamanin mulkin Buhari.

Hashim
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho
Hashim
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Rikicin Iran Da Amurka: Gabas Ta Tsakiya Ta Ɗauki Zafi

Rikicin Iran Da Amurka: Gabas Ta Tsakiya Ta Ɗauki Zafi

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.