ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

GDPn Nijeriya Ya Yi Ƙasa Fiye da Na Shekaru 20 da Suka Wuce A Zamanin Obasanjo — Hashim

by Bello Hamza and Sulaiman
7 months ago
Hashim

Wani ɗan takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Dr. Gbenga Hashim, ya soki yadda tattalin arzikin Nijeriya ke tafiya a ƙarƙashin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, yana mai cewa tattalin arzikin ƙasar ya fi rauni a yau idan aka kwatanta da lokacin mulkin tsofaffin shugabanni, musamman Olusegun Obasanjo da Goodluck Jonathan.

 

Hashim ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin wata tattaunawa kai tsaye a tashar Channels Television tare da Seun Okinbaloye, inda suka tattauna kan makomar tattalin arzikin Najeriya da kuma rawar da matasan Najeriya ke takawa a tattalin arzikin duniya, a shirin Politics Today.

ADVERTISEMENT
  • Kotun Amurka Ta Yanke Wa Wanda Yayi Yunƙurin Kashe Trump Hukuncin Ɗaurin Rai Da Rai
  • INEC Ta Amince Da Shugabancin PDP Tsagin Wike

Ya ce bayanan tattalin arziki na hukuma sun nuna cewa tsare-tsaren kuɗi da na kasafin kuɗi na gwamnatocin jam’iyyar APC a cikin shekaru goma da suka gabata sun gaza tafiya daidai da karuwar yawan jama’a da buƙatun ci gaba.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

“GDP a zamanin Obasanjo ya kai kusan dala biliyan 267. A zamanin Jonathan kuwa ya tashi zuwa sama da dala biliyan 574. Amma a yau, a ƙarƙashin Tinubu, ya faɗi zuwa kusan dala biliyan 230. Wannan koma baya ne mai tayar da hankali ga ƙasa mai yalwar albarkatun ɗan Adam da na ƙasa,” in ji Hashim.

 

Ɗan takarar na PDP ya kuma nuna damuwa kan faduwar darajar naira, yana mai cewa darajar da take da ita a halin yanzu ta yi ƙasa ƙwarai da abin da ya dace da tushen tattalin arzikin Najeriya. Ya ce hakan ya ƙara tsadar rayuwa tare da raunana gwiwar masu zuba jari.

 

Hashim, wanda shi ma ɗan kasuwa ne a matakin duniya, ya kuma tambayi irin gudunmawar da Shugaba Tinubu ya bayar wajen ci gaban jihar Lagos, yana kwatanta ta da ta tsohon shugaban soja, Janar Ibrahim Babangida (IBB). Ya ce Babangida ya fi bayar da gudunmawa mai ɗorewa ta hanyar gina Gadar Third Mainland.

 

“IBB ya fi ba da gudunmawa ga ci gaban Lagos saboda shi ne ya gina Gadar Third Mainland. Idan ka cire wannan gada a yau, me ya rage? Ƙaramar gadar Lekki da Tinubu ya gina kuma ya sanya kuɗin wucewa ba ta kai Third Mainland da IBB ya gina ba,” in ji Hashim.

 

Ya kuma yi watsi da jam’iyyar Action Democratic Congress (ADC) a matsayin wata sahihiyar madadin siyasa, yana cewa da dama daga cikin mambobinta suna da alaƙa da matsalolin tsaro da tattalin arziki da ƙasar ke fuskanta.

 

“Baya ga Peter Obi da watakila Atiku Abubakar, yawancin sauran ’yan ADC Buharawa ne da ake zargi da kasancewa cikin matsalar da muke ciki a yau,” in ji shi.

Hashim ya kalubalanci mambobin tawagar kula da tattalin arzikin gwamnatin Tinubu, ciki har da Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) da Ministan Kuɗi, da su fito fili su kare ayyukansu a muhawarar kai tsaye.

 

“Kalubale ne a fili — su fito da ƙwararrunsu, gwamnan CBN da ministan kuɗi, mu yi muhawara kai tsaye kan tattalin arziki,” in ji shi.

Yana mai jaddada cewa an rage darajar naira fiye da kima, Hashim ya ce karin yawan man fetur da ake samarwa daga kusan ganga 900,000 a rana zuwa kusan ganga miliyan 1.8, tare da raguwar shigo da man fetur sakamakon ƙarin tacewa a cikin gida, ya kamata su taimaka wajen ƙarfafa darajar naira, ba wai ta ci gaba da faduwa ba idan aka kwatanta da zamanin mulkin Buhari.

Hashim
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina
Hashim
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

Labarai

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Labarai

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Next Post
Rikicin Iran Da Amurka: Gabas Ta Tsakiya Ta Ɗauki Zafi

Rikicin Iran Da Amurka: Gabas Ta Tsakiya Ta Ɗauki Zafi

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.