ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

GDPn Nijeriya Ya Yi Ƙasa Fiye da Na Shekaru 20 da Suka Wuce A Zamanin Obasanjo — Hashim

by Bello Hamza and Sulaiman
6 months ago
Hashim

Wani ɗan takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Dr. Gbenga Hashim, ya soki yadda tattalin arzikin Nijeriya ke tafiya a ƙarƙashin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, yana mai cewa tattalin arzikin ƙasar ya fi rauni a yau idan aka kwatanta da lokacin mulkin tsofaffin shugabanni, musamman Olusegun Obasanjo da Goodluck Jonathan.

 

Hashim ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin wata tattaunawa kai tsaye a tashar Channels Television tare da Seun Okinbaloye, inda suka tattauna kan makomar tattalin arzikin Najeriya da kuma rawar da matasan Najeriya ke takawa a tattalin arzikin duniya, a shirin Politics Today.

ADVERTISEMENT
  • Kotun Amurka Ta Yanke Wa Wanda Yayi Yunƙurin Kashe Trump Hukuncin Ɗaurin Rai Da Rai
  • INEC Ta Amince Da Shugabancin PDP Tsagin Wike

Ya ce bayanan tattalin arziki na hukuma sun nuna cewa tsare-tsaren kuɗi da na kasafin kuɗi na gwamnatocin jam’iyyar APC a cikin shekaru goma da suka gabata sun gaza tafiya daidai da karuwar yawan jama’a da buƙatun ci gaba.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP

“GDP a zamanin Obasanjo ya kai kusan dala biliyan 267. A zamanin Jonathan kuwa ya tashi zuwa sama da dala biliyan 574. Amma a yau, a ƙarƙashin Tinubu, ya faɗi zuwa kusan dala biliyan 230. Wannan koma baya ne mai tayar da hankali ga ƙasa mai yalwar albarkatun ɗan Adam da na ƙasa,” in ji Hashim.

 

Ɗan takarar na PDP ya kuma nuna damuwa kan faduwar darajar naira, yana mai cewa darajar da take da ita a halin yanzu ta yi ƙasa ƙwarai da abin da ya dace da tushen tattalin arzikin Najeriya. Ya ce hakan ya ƙara tsadar rayuwa tare da raunana gwiwar masu zuba jari.

 

Hashim, wanda shi ma ɗan kasuwa ne a matakin duniya, ya kuma tambayi irin gudunmawar da Shugaba Tinubu ya bayar wajen ci gaban jihar Lagos, yana kwatanta ta da ta tsohon shugaban soja, Janar Ibrahim Babangida (IBB). Ya ce Babangida ya fi bayar da gudunmawa mai ɗorewa ta hanyar gina Gadar Third Mainland.

 

“IBB ya fi ba da gudunmawa ga ci gaban Lagos saboda shi ne ya gina Gadar Third Mainland. Idan ka cire wannan gada a yau, me ya rage? Ƙaramar gadar Lekki da Tinubu ya gina kuma ya sanya kuɗin wucewa ba ta kai Third Mainland da IBB ya gina ba,” in ji Hashim.

 

Ya kuma yi watsi da jam’iyyar Action Democratic Congress (ADC) a matsayin wata sahihiyar madadin siyasa, yana cewa da dama daga cikin mambobinta suna da alaƙa da matsalolin tsaro da tattalin arziki da ƙasar ke fuskanta.

 

“Baya ga Peter Obi da watakila Atiku Abubakar, yawancin sauran ’yan ADC Buharawa ne da ake zargi da kasancewa cikin matsalar da muke ciki a yau,” in ji shi.

Hashim ya kalubalanci mambobin tawagar kula da tattalin arzikin gwamnatin Tinubu, ciki har da Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) da Ministan Kuɗi, da su fito fili su kare ayyukansu a muhawarar kai tsaye.

 

“Kalubale ne a fili — su fito da ƙwararrunsu, gwamnan CBN da ministan kuɗi, mu yi muhawara kai tsaye kan tattalin arziki,” in ji shi.

Yana mai jaddada cewa an rage darajar naira fiye da kima, Hashim ya ce karin yawan man fetur da ake samarwa daga kusan ganga 900,000 a rana zuwa kusan ganga miliyan 1.8, tare da raguwar shigo da man fetur sakamakon ƙarin tacewa a cikin gida, ya kamata su taimaka wajen ƙarfafa darajar naira, ba wai ta ci gaba da faduwa ba idan aka kwatanta da zamanin mulkin Buhari.

Hashim
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
Hashim
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal
  • Sulaiman
    Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba
  • Sulaiman
    An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
  • Sulaiman
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

MASU ALAKA

Hashim
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

July 25, 2026
Hashim
Labarai

Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP

July 25, 2026
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe
Rahotonni

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

July 25, 2026
Next Post
Rikicin Iran Da Amurka: Gabas Ta Tsakiya Ta Ɗauki Zafi

Rikicin Iran Da Amurka: Gabas Ta Tsakiya Ta Ɗauki Zafi

LABARAI MASU NASABA

Tsakanin Digiri Da Sana’a Wanne Ya Fi Muhimmanci A Wannan Lokacin?

Tsakanin Digiri Da Sana’a Wanne Ya Fi Muhimmanci A Wannan Lokacin?

July 25, 2026
Hashim

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

July 25, 2026
Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

July 25, 2026
Hashim

Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP

July 25, 2026
Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

July 25, 2026
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

July 25, 2026
Hashim

Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu

July 25, 2026
Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

July 25, 2026
Hashim

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

July 25, 2026
Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.