Aƙalla mutum 16 ne gini ya rufta a kansu a unguwar Dan Dishe, Kwanar Yashi, da ke Ƙaramar Hukumar Dala a Jihar Kano.
Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano ta ce lamarin ya faru da misalin ƙarfe 4:32 na safiyar ranar Asabar.
Kakakin hukumar, Saminu Yusuf Abdullahi, ya ce jami’an hukumar sun garzaya wurin bayan sun samu kiran gaggawa.
Ya ce bayan isar su, jami’an sun tarar da wani gini ya rufta, inda ya danne mutum 16.
A cewar hukumar, an yi nasarar ceto mutum 13 da ransu, ciki har da wani yaro mai shekaru 15, Al-Mustapha Yusuf, Khadija Yusuf mai shekaru bakwai da wasu yara.
Sai dai Affan Yusuf mai shekaru biyar, Hassana Yusuf mai shekaru bakwai da Ummulkursum Yusuf ɗan wata tara, an ceto su a sume.
Hukumar ta ce an miƙa dukkanin mutanen da aka ceto ga Usman Ibrahim, wanda aka bayyana a matsayin ɗan uwan mahaifinsu, domin ɗaukar matakan da suka dace.
Har yanzu ba a gano musabbabin ruftawar ginin ba, yayin da hukumar ta ce tana ci gaba da bincike.
Hukumar ta kuma yi kira ga jama’a da su ƙara yin taka-tsantsan tare da bin matakan tsaro, musamman a lokacin damuna, domin rage hatsarin ruftawar gine-gine.














